Tinubu Ya Shirya Yiwa Majalisar Ministoci Garambawul, Za a Runtuma Kora

Tinubu Ya Shirya Yiwa Majalisar Ministoci Garambawul, Za a Runtuma Kora

  • Alamu na nuna cewa wasu daga cikin monistocin da ke cikin gwamanatin Shugaba Bola Tinubi za su rasa kujerunsu
  • Wata majiya daga fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa Shugaba Tinubu ya shirya tsaf domin yiwa majalisar ministocinsa garambawul
  • Majiyar ta nuna cewa shugaban ƙasan bai gamsu da kamun ludayin wasu daga cikin ministocin ba kuma a shirye yake ya kore su daga muƙamin su

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Akwai yiwuwar shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yiwa majalisar ministocinsa garambawul.

Idan ba wani sauyi aka samu ba, Shugaba Tinubu zai yi garambawul ɗin ne a cikin sati mai zuwa.

Tinubu zai kori ministoci
Akwai yiwuwar Tinubu ya kori wasi ministoci Hoto: @DOlusegun
Source: Facebook

Jaridar Tribune ta rahoto cewa wata majiya mai tushe a fadar shugaban ƙasa ta ce garambawul ɗin za a yi shi ne domin a kawo sababbin fuskokin da za su ƙara ɗaga darajar gwamnati.

Kara karanta wannan

Jigon APC ya gayawa Shugaba Tinubu gaskiya kan tsadar rayuwa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yaushe Tinubu zai yi garambawul?

Majiyar ta bayyana cewa akwai yiwuwar Tinubu ya yi garambawul ɗin kafin ya tafin taron majalisar ɗinkin duniya (UNGA) wanda za a yi a birnin New York a cikin sati mai zuwa.

Majiyar ta ce Shugaba Tinubu yana sane da ƙorafe-ƙorafen da ake yi na rashin kataɓus ɗin wasu ministocinsa kuma a shirya yake ya sallame su.

Majalisar ta ƙara da cewa an kammala haɗa jerin sunayen ministocin da za a kora daga gwamnatin.

"Shugaba Tinubu bai gamsu da kataɓus ɗin wasu daga cikin ministocinsa ba kuma a shirye yake ya sallame su."
"Bayan ya dawo daga taron UNGA, shugaban ƙasa zai kafa sabuwar majalisar ministoci."

- Wata majiya

Jaridar ta ƙara da cewa wani tsohon minista a gwamnatin Muhammadu Buhari na daga cikin waɗanda ake sa ran ba muƙamin minista.

Jigo a APC ya ba Tinubu shawara

A wani labarin kuma, kun ji cewa wani jigo a jam'iyyar APC a jihar Osun, Olatunbosun Oyintiloye, ya ba shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu shawara.

Kara karanta wannan

Ajuri Ngelale: Kura kurai 2 da suka sa hadimin Tinubu ya ajiye aikinsa

Olatunbosun Oyintiloye ya buƙaci Shugaba Tinubu da ya gaggauta cire ƴan Najeriya daga cikin halin ƙuncin da suka tsinci kansu a ciki.

Olatunbosun Oyintiloye ya nuna cewa ƴan Najeriya na shan wuya wanda hakan ya sanya dole shugaban ƙasan ya ɗauki matakan kawo musu ɗauki

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng