"Ka da Ku Ɗagawa Kowa Ƙafa," Gwamma Abba Ya Kafa Kwamiti kan Abin da Ya Faru a Kano

"Ka da Ku Ɗagawa Kowa Ƙafa," Gwamma Abba Ya Kafa Kwamiti kan Abin da Ya Faru a Kano

  • Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da kwamitin da zai gudanar da bincike kan abubuwan da suka faru lokacin zanga-zanga
  • Gwamnan Abba ya buƙaci 'yan kwamitin su ji tsoron Allah wajen sauke nauyin da aka ɗora masu kuma su yi aiki ba sani ba sabo
  • Kano na cikin jihohin da zanga-zanga ta yi zafi, bara gurbi sun lalata tare da sace kayayyakin gwamnati da na ƴan kasuwa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano - Gwamna Abba Kabir Yusuf na Kano ya kafa kwamitin shari'a wanda zai gudanar da bincike kan abubuwan da suka faru lokacin zanga-zangar 1 zuwa 10 ga watan Agusta.

Kwamitin zai gudanar da bincike mai zurfi kan asarar rayuka, ɓarnatar da dukiyar al'umma wanda aka yi a lokacin zanga-zangar gama gari.

Kara karanta wannan

Mahaifiyar tsohon shugaba Yar'adua, Hajiya Dada ta riga mu gidan gaskiya

Gwamna Abba Kabir Yusuf.
Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya kafa kwamitk kan abubuwan da suka auku lokacin zanga-zanga Hoto: Abba Kabir Yusuf
Asali: Twitter

Abba ya ba kwamitin cikakkiyar dama

Hakan na kunshe a wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Litinin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Abba ya buƙaci mambobin kwamitin su yi aiki ba sani ba sabo kuma kar su ɗaga wa kowa ƙafa matuƙar suka gano yana da hannu a ɓarnar da aka yi.

Abba Kabir ya faɗawa ƴan kwamitin haka ne a lokacin da yake kaddamar da su a fadar gwamnatinsa da ke birnin Kano.

Gwamna ya ja hankalin ƴan kwamitin

A jawabinsa, Gwamna Abba ya ce:

"Ina amfani da wannan damar wajen sake jaddada cewa mun shirya kuma muna da ƙwarin guiwa za mu iya tunkarar komai kan gaskiyar mu ba tare da la'akari da mai zai je ya dawo ba."
"Saboda haka a madadin gwamnati da ɗaukacin al'ummar jihar Kano muna kira gare ku da ku yi kokarin sauke nauyin da aka ɗora maku cikin gaskiya da jajircewa."

Kara karanta wannan

Gwamna Abba ya sake rusa aikin Ganduje, ya maido makarantun kwanan mata 15

Abba ya bude makarantun da Ganduje ya rufe

A wani rahoton kuma, an ji Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dawo da makarantun kwana 15 na mata waɗanda Abdullahi Ganduje ya soke a zamaninsa.

Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa tuni shirye-shirye suka yi nisa na sake mayar da makarantun na kwana kamar yadda aka sansu a baya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262