Ana Fama da Yunwa, Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ɓarna a Gonakin Mutane a Jihohi 2 na Arewa

Ana Fama da Yunwa, Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ɓarna a Gonakin Mutane a Jihohi 2 na Arewa

  • Rahotanni sun nuna ambaliyar ruwa ta yi kaca-kaca da amfanin gonakin al'umma a wasu yankuna da ke jihohin Kebbi da Neja
  • Hukumar N-HYPPADEC ta miƙa sakon jaje ga waɗanda ibtila'in ya shafa tare da yabawa matakin gwamnatin tarayya na ware N3bn
  • Najeriya na fama da ambaliyar ruwa kusan kowace shekara a jihohi da dama musamman waɗanda ruwa ya gitta ta cikinsu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Ibtila'in ambaliyar ruwa ya lalata amfanin gonakin al'umma a karamar hukumar Argungu da wasu yankunan da dama a jihohin Kebbi da Neja.

Shugaban sashin hulɗa da jama’a na Hukumar bunƙasa wutar lantarki ta ƙasa (N-HYPPADEC), Nura Wakili ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata. 

Kara karanta wannan

Gwamna a Arewa zai rage yawan masu zaman kashe wando, zai ɗauki ma'aikata

Ibtila'in ambaliyar ruwa a Najeriya.
Ambaliyar ruwa ta lalata amfanin gonaki a jihohin Neja da Kebbi Hoto: Mustapha Muhammad Gujber
Asali: Facebook

Nura Wakil ya miƙa sakon jaje a madadin hukumar zuwa mazauna yankunan da abin da ga shafa musamman manoma, kamar yadda Channels tv ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ambaliya ta jawo koma baya

Hukumar ta ayyana lamarin a matsayin wani gagarumin koma baya ga kokarin da Najeriya ke yi na samar da wadatar abinci mai ɗorewa.

Sanarwar ta ce, Manajan Daraktan Hukumar, Abubakar Yelwa, ya nuna matukar damuwarsa kan yadda ambaliyar ruwan ta shafi rayuwar al’ummar da dama.

Ya kuma yabawa gwamnatin tarayya bisa matakin gaggawar da ta dauka na ware ₦3bn domin tallafawa wadanda ibtila'in ya rutsa da su.

Yadda aka riƙa wayar da kan manoma

A baya dai hukumar ta gudanar da gangamin wayar da kan jama’a ta kafafen yada labarai da ziyara wanda hakan ya taimaka wajen rage illar da ambaliyar ruwa ke yi.

Sai dai duk da haka ambaliyar ta ɓarnata amfanin gonaki masu ɗumbin yawamusamman waɗanda ke kusa da ruwa.

Kara karanta wannan

Ambaliya: Ministan Tinubu ya fadi yadda Najeriya za ta shawo kan karancin abinci

N-HYPPADEC ta jaddada bukatar mutane su yi taka tsan-tsan kuma su ɗauki matakan kariya a yankunansu tun kafin faruwar irin haka, rahoton Guardian.

Gwamnatin Kwara za ta ɗauki ma'aikata

A wani rahoton gwamnatin jihar Kwara karkashin Gwamna Abdulrahman Abdulrazaq ta ce za ta ɗauki sababbin malaman makaranta da ma'aikata 1,600.

Shugaban hukumar ilimin bai ɗaya SUBEB, Farfesa Raheem Adaramaja ya ce za a ɗauki ma'aikatan nr domin cike gurbin waɗanda suka yi ritaya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262