NAHCON: Bola Tinubu Ya Naɗa Shugaban Izala a Muƙamin Gwamnatin Tarayya

NAHCON: Bola Tinubu Ya Naɗa Shugaban Izala a Muƙamin Gwamnatin Tarayya

  • Bola Ahmed Tinubu ya naɗa shugaban Izala reshen Kano, Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan a matsayin sabon shugaban hukumar alhazai
  • Shugaban ƙasar ya yi wannan naɗi ne bayan ya tsige Jalal Arabi, wanda EFCC ke bincika kan zargin karkatar da kuɗin tallafin hajjin bana 2024
  • Mai magana da yuwun shugaban ƙasa, Ajuri Ngelale ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar da yammacin yau Litinin

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya nada Sheikh Farfesa Abdullahi Saleh Usman (Pakistan) a matsayin Shugaban Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON).

Hakan na zuwa ne bayan shugaban ƙasar ta sauke Jalal Ahmad Arabi daga matsayin shugaban NAHCON kan badaƙalar tallafin hajjin 2024.

Kara karanta wannan

Atiku ya yi zazzafan martani ga Shugaba Tinubu kan dawo da tallafin man fetur

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu.
Bola Tinubu ya nada Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan a matsayin shugaban NAHCON Hoto: Ajuri Ngelale
Asali: Facebook

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Ajuri Ngelale ne ya sanar da naɗin Sheikh Pakistan a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Litinin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Taƙaitaccen bayani kan Sheikh Pakistan

Farfesa Saleh Pakistan, fitaccen malamin Sunnah a Najeriya ya yi karatu a Jami’ar Madina da ke ƙasa mai tsarki da Jami’ar Peshawar da ke Pakistan.

Malamin yana da kwarewa a harkokin da suka shafi aikin Hajji kasancewar ya jagoranci hukumar jin daɗin alhazai ta jihar Kano a baya.

Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan shi ne shugaban ƙungiyar addinin Musulunci JIBWIS da aka fi sani da Izala ta reshen jihar Kano.

Bola Tinubu ya aikawa Pakistan sako

A sanarwar da Ngelale ya fitar, Shugaba Tinubu ya buƙaci Sheikh Pakistan ya yi ƙoƙarin sauke nauyin da Allah ya ɗora masa a wannna muƙami cikin gaskiya da rikon amana.

Kara karanta wannan

Kwanaki 3 da dawowa Najeriya, Tinubu zai sake lulawa kasar waje

“Shugaba Bola Tinubu ya amince da nadin Farfesa Abdullahi Saleh Usman a matsayin shugaban hukumar alhazai ta kasa NAHCON.
"Farfesa Abdullahi, babban malami ne wanda ya yi karatu makarantun Musulunci, Jami'ar Madinah da Jami'ar Peshawar ta Pakistan," in ji sanarwar.

NAHCON ta kama jigilar alhazai

A wani rahoton kuma Hukumar Alhazai ta ƙasa (NAHCON) ta kawo ƙarshen aikin jigilar Alhazan Najeriya daga ƙasa mai tsarki zuwa gida.

Jirgin ƙarshe wanda yake ɗauke da Alhazan jihar Kwara ya baro ƙasa mai tsarki a ranar Talata, 16 ga watan Yulin 2024.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262