Gwamna Ya Yi Muhimmin Abin Alheri Yayin da Jirgi Ya Halaka Bayin Allah a Arewa

Gwamna Ya Yi Muhimmin Abin Alheri Yayin da Jirgi Ya Halaka Bayin Allah a Arewa

  • Gwamnan jihar Sakkwato Ahmed Aliyu ya ware tallafin N30m ga waɗanda hatsarin jirgin ruwa ya rutsa da su a kauyen Dundaye
  • Gwamnan ya ce gwamnatinsa za ta bai wa iyalan mutum biyar da suka rasu a haɗarin N15m yayin da waɗanda suka tsira kuma za a ba su N15m
  • Ya ce zai samar da jiragen ruwa na zamani da rigunan ruwa domin kare rayukan al'umma a lokacin da suke tafiya a ruwa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Jigawa - Gwamna Ahmed Aliyu na Sokoto ya bayar da gudunmawar kudi N30m ga iyalan wadanda hatsarin jirgin ruwa ya rutsa da su a ƙauyen Dundaye. 

Idan baku manta ba a ƙarshen makon da ya gabata, wani kwale-kwale ya kife a kauyen Dundaye da ke karamar hukumar Wamakko a jihar Sakkwato.

Kara karanta wannan

Gwamna a Arewa ya yi amai ya lashe kan fara biyan ma'aikata sabon albashin N70,000

Gwamna Ahmed Aliyu na jihar Sokoto.
Gwamna Aliyu ya ba da tallafin N30m ga wadan hatsarin jirgi ya shafa a Sokoto Hoto: Ahmed Aliyu
Asali: Facebook

Rahoton Tribune Nigeria ya nuna cewa haɗarin jirgin ya laƙume rayukan mutum biyar, yayin da sauran kuma aka samu nasarar ceto su da rai.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Aliyu ya ba da kyautar N30m

Da yake sanar da bayar da tallafin, Gwamna Aliyu ya ce gwamnatinsa za ta ba iyalan waɗanda Allah ya yiwa rasuwa a hatsarin N15m

Gwamnan ya ƙara da cewa waɗanda Allah ya yiwa gyaɗar dogo suka tsira daga haɗarin, za su samu N15m, jimulla N30m kenan.

Gwamnatin Sokoto za ta sayo jiragen zamani

Ya kuma bayyana cewa gwamnatin jihar za ta samar da jiragen ruwa na zamani da rigunan ruwa domin tabbatar da kariya ga al'umma idan suka shiga ruwan.

Ahmed Aliyu ya ce:

"Ina ƙara kashedi ga masu jirgin ruwa su daina sakaci a lokacin da suka ɗauko mutane, na samu labarin gangancin direba ne ya jawo haɗarin, don Allah ku daina."

Kara karanta wannan

Gwamna ya jingine Atiku, ya faɗi mutum 1 da ya kamata ya karɓi mulkin Najeriya a 2027

Ahmed Aliyu ya ba mazauna shawara

Gwamna Aliyu ya buƙaci mutanen da ke rayuwa a kewayen tafkin ɗa su yi amfani da damar wajen yin noman rani da sauran ayyukan noma da ruwan.

A cewar gwamnan, hakan zai taimaka wajen samar da isasshen abinci a jihar Sakkwato da ma ƙaa baki ɗaya.

Jigawa ta fara rabon tallafin Tinubu

Kun ji cewa Gwamna Umar Namadi ya kaddamar da fara rabon tallafin buhunan shinkafa, masara, dawa da gero ga masu ƙaramin ƙarfi a Jigawa.

Gwamnan ya bayyana cewa za a raba tallafin a dukkan gundumomi 187 da ke ƙananan hukumomi 27 a jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262