Gwamna Ya Cika Alkawari, Ya Fara Rabawa Talakawa Tallafin Buhunan Shinkafa da Masara

Gwamna Ya Cika Alkawari, Ya Fara Rabawa Talakawa Tallafin Buhunan Shinkafa da Masara

  • Gwamna Umar Namadi ya kaddamar da fara rabon tallafin buhunan shinkafa, masara, dawa da gero ga masu ƙaramin ƙarfi a Jigawa
  • Gwamnan ya bayyana cewa za a raba tallafin a dukkan gundumomi 187 da ke ƙananan hukumomi 27 a jihar
  • Da yake jawabi a wurin taron kaddamarwa, gwamnan ya ce kayan tallafin sun fito ne daga gwamnatin tarayya don a rabawa mabukata

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Jigawa - Gwamnatin jihar Jigawa ta kaddamar da rabon buhunan shinkafa 59,000 mai nauyin kilogiram 25 da hatsi iri-iri ga marasa galihu a faɗin jihar.

Gwamnatin jihar ta fara rabon waɗannan kayayyakin abinci ga maɓukata da marasa galihu a gundumomi 287 da ke ƙananan hukumomi 27 a Jigawa.

Kara karanta wannan

Manyan ƴan siyasa, tsofaffin hadiman Ganduje sun kafa kungiya da manufa 1 a Kano

Gwamna Umar Namadi.
Gwamnatin Jigawa ta fara raba shinkafa da masara ga marasa galihu Hoto: Umar Namadi
Asali: Twitter

Gwamna Umar Namadi Ɗanmodi ne ya jagoranci ƙaddamar da fara rabon tallafin abincin a gidan gwamnati da ke birnin Dutse, kamar yadda Leadership ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnatin Tinubu ta kai tallafi Jigawa

Da yake jawabi a wurin taron, Gwamnan Namadi ya ce gwamnatin tarayya karƙashin Bola Ahmed Tinubu ce ta turo kayan abincin don a rabawa jama'a.

Ya ce kayayyakin abincin da za a raba sun hada da buhunan dawa 13,825, buhunan gero 9,500, buhunan masara 11,500 da buhunan shinkafa 24,000.

Umar Namadi ya ce:

“Domin tabbatar da tallafin ya shiga gidaje da yawa, gwamnatin jiha ta ƙara da katan 23,000 na taliyar yara, buhunan shinkafa 5,000, dawa 500 da buhunan masara 5,000.

Yadda talakawan Jigawa za su amfana

Kwamishinan ayyuka na musamman Hon. Auwal Dalladi Sankara, ya ce an zabo wadanda za su ci gajiyar wannan tallafi daga kananan hukumomi 27 na jihar.

Kara karanta wannan

Gwamna ya jingine Atiku, ya faɗi mutum 1 da ya kamata ya karɓi mulkin Najeriya a 2027

Ya ce rabon kayan abinci ci gaba ne da wasu tsare-tsare na tallafi da Gwamna Umar Namadi ya aiwatar wanda sama da mutane miliyan uku suka amfana.

Wani matashi ɗan Jigawa, Aminu Majeh ya bayyana cewa a kwanakin baya gwamnati ta raba tallafi kuma abin farin cikin ko baka san kowa ba za ka samu.

Aminu ya shaidawa Legit Hausa cewa yana fatan wannan karon ma ka da a sanya siyasa a rabon saboda kowa ya san matsanancin halin kuncin da ake ciki.

"A zahirin gaskiya gwamnatin Ɗanmodi tana kamantawa wajen raba kayan tallafi irin wannan, duk da ban samu ba amma maƙocin mu ya samu, mabuƙata da dama sun samu.
"Ina fatan wannan karon ma ba za a maida abin siyasa ba, domin da zaran an sa siyasa to komai ya lalace. Wallahi mutane na cikin yunwa da wahala Allah ya yaye mana," in ji shi.

Gwamnan Kano ya naɗa kwamishinan tsaro

Kara karanta wannan

Gwamna ya karya farashin buhun shinkafa zuwa N40,000 a Arewa, bayanai sun fito

A wani rahoton kuma Gwamna Abba Kabir ya naɗa Manjo Janar Muhammad Inuwa Idris mai ritaya a matsayin sabon kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida

Abba Kabir ya sanar da wannan naɗin ne a wurin rantsar da majalisun gudanarwa da jami'o'i da manyan makarantu na jihar Kano.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262