'Yan Bindiga Sun Sace Kwamishina da Matarsa a Hanyar Zuwa Ɗaura Auren Ɗiyar Gwamna

'Yan Bindiga Sun Sace Kwamishina da Matarsa a Hanyar Zuwa Ɗaura Auren Ɗiyar Gwamna

  • Ƴan bindiga sun yi garkuwa da kwamishinan matasa na jihar Anambra, Agha Mba tare da matarsa a hanyarsu ta zuwa Abuja
  • Rahotanni sun nuna cewa kwamishinan ya shiga hannun masu garkuwa ne a hanyar zuwa ɗaurin auren ɗiyar Gwamna Charles Soludo
  • Sakataren yaɗa labaran gwamnan Anambra ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce gwamnati ta umarci jami'an tsaro su fara bincike nan take

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Anambra - Rahotannin da ke shigowa sun nuna cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da kwamishinan matasa na jihar Anambra, Agha MBA, tare da matarsa.

An tattaro cewa an kashe daya daga cikin hadimansa dan garin Onitsha a lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa daurin auren diyar Gwamna Charles Chukwuma Soludo.

Kara karanta wannan

Kwamishinan da 'yan bindiga suka sace kan hanyar zuwa daurin aure ya kubuta

Farfesa Charles Soludo.
Ana fargabar ƴan bindiga sun yi awon gaba da kwamishinan matasa na jihar Anambra Hoto: Charles Chikwuma Soludo
Asali: Twitter

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a ranar Juma’a, 16 ga watan Agusta, 2024 yayin da yake hanyar zuwa babban birnin tarayya Abuja.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bayanai sun nuna maharan sun sace kwamishinan da mai ɗakinsa a yankin jihar Kogi, suna hanyar zuwa ɗaura auren ɗiyar Gwamna Soludo, wanda za a yi ranar Asabar.

Gwamnatin Anambra ta tabbatar da lamarin

Sakataren yaɗa labaran gwamnan jihar Anambra, Christian Aburime, ya tabbatar da faruwar lamarin inji rahoton Channels tv.

Ya ce har yanzu gwamnati ba ta gano ainihin wurin da aka sace kwamishinan ba amma dai an ambaci wurare biyu, Ubiaja a jihar Edo da kuma jihar Kogi.

Gwamna Soludo ya fara ɗaukar mataki

Ya ce Gwamna Soludo ya fara tuntubar jami’an tsaro don ganin an ceto kwamishinan da matarsa ​​cikin ƙoshin lafiya kuma ba tare da jan lokaci ba.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun kai hari ana tsakiyar shagalin biki, sun tafka mummunar ɓarna

Aburime ya ce:

“Tuni Oga (Gwamna Soludo) ya fara tuntubar jami’an tsaro don tabbatar da an ceto Kwamishinan da matarsa ​​cikin ƙoshin lafiya kuma ba tare da ɓata lokaci ba."

Yan bindiga sun tashi bom a Anambra

Kun ji cewa ƴan bindiga sun kai mummunan hari kan ƴan sanda a shingen binciken ababen hawa a jihar Anambra da ke Kudu maso Gabas.

Rundunar ƴan sanda ta ce maharan sun yi amfani da bom suka kashe ɗan sanda ɗaya a harin tare da jikkata wani mutum ɗaya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262