Katsina: Gwamna Ya Sauya Dokar da Ya Sanya Lokacin Zanga Zanga a Najeriya

Katsina: Gwamna Ya Sauya Dokar da Ya Sanya Lokacin Zanga Zanga a Najeriya

  • Muƙaddashin gwamnan Katsina, Farouk Lawal Jobe ya cire dokar hana fita da aka sanya a ƙananan hukumomin jihar
  • Sakataren gwamnatin Katsina, Abdullahi Faskari ne ya bayyana hakan ranar Talata, ya ce mutane na da damar ci gaba da harkokinsu
  • Katsina dai na ɗaya daga cikin jihohin da aka samu tashe-tashen hankula a lokacin zanga-zangar adawa da manufofin gwamnati

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Katsina - Gwamnatin jihar Katsina da ke Arewa maso Yammacin Najeriya ta janye dokar hana fita da ta sanya sakamakon rikice-rikicen da suka faru a wasu sassa.

Sakataren gwamnatin jihar, Abdullahi Faskari ne ya bayyana hakan a wata sanarwa ranar Talata, 13 ga watan Agusta, 2024.

Kara karanta wannan

Bayan gama zanga zanga, gwamna a Arewa ya ɗauko hanyar share hawayen talakawa

Farouk Lawal Jobe.
Gwamnatin Katsina ta cire dokar zaman gida da ta sanya lokacin zanga zanga Hoto: Farouk Lawal Jobe
Asali: Facebook

Idan ba ku manta ba mukaɗdashin gwamnan jihar Katsina, Farouk Jobe ya sa dokar hana fita saboda tashin-tashinar da aka yi lokacin zanga-zanga, Channels tv ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Masu zanga-zanga sun yi ɓarna

Katsina dai na daya daga cikin jihohin da aka yi tashe-tashen hankula a lokacin zanga-zanga kan tsadar rayuwa wadda masu shiryawa suka ce ta lumana ce.

A rahoton The Nation, masu zanga-zangar sun yi kira ga gwamnatin tarayya karkashin shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta sauya tunani kan wasu manufofi kamar cire tallafin mai.

Sai dai tun a ranar farko, zanga-zangar da rikiɗa ta koma tashin hankali yayin da ƴan daba da ake zargin sun shiga cikin masu zanga-zangar suka riƙa aikata laifuka.

Masu zanga-zangar dai sun riƙa bankawa wurare wuta tare da sace-sacen dukiyar al'umma da barnata kayan gwamnati, lamarin da ya sa mahukunta suka ɗauki mataki.

Kara karanta wannan

Mutane sun ƙara samun sauƙi bayan tashin tashinar masu zanga zanga a Arewa

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta sanar da kama mutane 64 da ake zargi da wawure dukiyar jama’a da barna a lokacin zanga-zangar da aka yi a fadin kasar.

Gwamnatin Katsina ta janye doka

Da yake sanar da cire dokar hana fita, sakataren gwamnatin Katsina ya ce an ɗauki wannan matakin ne domin bai wa jama'a damar ci gaba da harkokinsu.

Wani matashi da ya so fita zanga-zanga a Katsina amma ya fasa saboda abin da ya faru, Mubarak Lawal ya shaida mana cewa matasa sun ɓata rawarsu da tsalle.

Da yake zantawa da wakilin Legit Hausa, matashin ya ce wannan ba ita ce hanyar da ya kamata ƴan Najeriya musamman ƴan uwansa matasa su nuna fushinsu ba.

"Abubuwan da suka faru ba wai a nan Katsina kaɗai ba a dukkan jihohi sun nuna ba zanga-zangar neman ƴanci muka yi ba, ɓarna da sace-sace kawai aka yi.
"Na so shiga wannan zanga-zanga amma tunda na fahimci ba za a kare lafiya ba na janye kaina, ba zai yiwu na shiga na jawo ma kaina wata matsala ba," in ji shi.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Tsohon gwamnan Kano ya gano bakin zaren, ya aika saƙo ga Tinubu

An cire dokar hana fita a Jigawa

A wani labarin gwamnatin jihar Jigawa ƙarƙashin jagorancin Gwamna Umar Namadi, ta cire dokar hana fita da ta sanya a ƙananan hukumomi takwas na jihar.

Dokar hana fitan da aka sanya sakamakon rikicin da aka samu a lokacin zanga-zangar nuna adawa da halin ƙunci, yanzu an cire ta gaba ɗaya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262