Zanga zanga: Ƙasar Poland Ta Fara Kamun Ƙafa domin a Saki mutanenta da Aka Kama a Kano

Zanga zanga: Ƙasar Poland Ta Fara Kamun Ƙafa domin a Saki mutanenta da Aka Kama a Kano

  • Ƙasar Poland ta roƙi Najeriya ta haƙura da saki ƴan ƙasarta da aka kama da laifin ɗaga tutocin Rasha lokacin zanga-zanga a Kano
  • Mataimakin ministan harkokin wajen ƙasar, Jakub Wisniewski ya ce ƴan Poland bakwai da aka kama sun aikata laifin ne cikin jahilci
  • Jami'an DSS dai sun tabbatar da cafke mutum bakwai ƴan asalin kasar Poland da ke nahiyar Turai bisa zargin ɗaga tutar Rasha yayin zanga-zanga

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Gwamnatin kasar Poland ta roki Najeriya ta saki ‘yan ƙasarta bakwai da aka kama a Kano bisa zargin ɗaga tutar Rasha yayin zanga-zangar yunwa da aka yi.

Mataimakin ministan harkokin wajen Poland, Jakub Wisniewski ne ya yi wannan roko yayin ganawa da jami'an diflomasiyyar Najeriya a birnin Warsaw.

Kara karanta wannan

Daga karshe 'yan sanda sun bayyana dalilin kai samame a hedkwatar kungiyar NLC

Masu ɗaga tutar Rasha.
Poland ta roki gwamnatin Najeriya ta saki ƴan kasarta da ta kama suna ɗaga tutar Rasha a lokacin zanga zanga Hoto: Khalipha Umar
Asali: Facebook

Ya roƙi gwamnatin Najeriya karkahin Bola Ahmed Tinubu ta yi hakuri da saƙi ƴan ƙasar Poland bakwai da aka kama, lakcara da ɗalibai shida, The Nation ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Poland ya roki alfarmar Najeriya

Ya ce waɗanda jami'an tsaron Najeriya suka kama sun shigo Najeriya ne daga jami'ar Warsaw domin halartar taron harshen Hausa.

"A taron na yi bayanin cewa na gamsu ɗaliban sun yi kuskure kuma ɗabi'arsu ta nuna sun aikata haka ne saboda rashin sanin al'adu da dokokin cikin gida a Najeriya.
"Ina rokon mahukunta su duba yiwuwar sako su, su dawo Poland zuwa cikin iyalansu domin danginsu sun ƙagu su sake haɗuwa da ƴan uwansu," in ji Wisniewski."

Alaƙar Polanda da Rasha

Amma Wisniewski ya ƙi yarda cewa ɗaliban sun ɗaga tutocin Rasha a fili saboda ba kasafai ake samun masu goyon bayan Rasha ba a ƙasar Poland, rahoton Notes Poland.

Kara karanta wannan

NLC ta yi martani mai zafi bayan jami'an tsaro sun kai samame a hedkwatarta

Poland da ke tsakiyar Turai ba za ta manta da lokacin da take a ƙarƙashin mulkin Rasha ba kuma 'yan kasar sun yi suka kan abin da suke kallo a matsayin zaluncin Rasha a Ukraine.

Wisniewski ya ƙara da cewa ƴan Poland bakwai da DSS ta kama an maida su Abuja kuma suna cikin koshin lafiya, yana mai rokon gwamnati ta taimaka ta sake su.

Shekarau ya ba Tinubu shawara

Kuna da labarin cewa Malam Ibrahim Shekarau ya buƙaci gwamnatin Bola Tinubu ta sake nazari kan manufofin tattalin arzikin da ta aiwatar tun bayan hawa mulki.

Tsohon gwamnan Kano ya ce lokaci ya yi da Shugaba Tinubu da hadimansa za su waiwayi baya, su amince da kura-kuransu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262