Shugaban NOA Ya Faɗi Matsalar da Za a Shiga Idan Aka Dawo da Tallafin Fetur

Shugaban NOA Ya Faɗi Matsalar da Za a Shiga Idan Aka Dawo da Tallafin Fetur

  • Darakta Janar na hukumar wayar da kan al'umma ya ce dawo da tallafin fetur ba zai yaye wa mutane talaucin da ake ciki ba
  • Lanre Issa-Onilu ya buƙaci ƴan Najeriya su lalubo dabarun da za su taimaka masu a rayuwa bayan tuge tallafin man fetur
  • Maido da tallafin na ɗaya daga cikin manyan buƙatun masu zanga-zanga wanda tuni shugaban ƙasa ya ce ba zai yiwu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Darakta-Janar na hukumar wayar da kan jama’a ta kasa (NOA), Lanre Issa-Onilu, ya yi fatali da baƙatar dawo da tallafin man fetur a Najeriya.

Issa-Onilu ya bayyana cewa dawo da tallafin ba zai warware wahalar da ake ciki ba illa ya ƙara jefa mutane cikin baƙin talauci.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Sojojin Najeriya sun yi magana kan kifar da gwamnatin Bola Tinubu

Gidan mai.
Dawo da tallafin mai ba zai magance wahalar da ƴan Najeriya ke ciki ba, in ji DG na NOA Hoto: NNPCL
Asali: Facebook

Tinubu ya kore dawo da tallafin fetur

Daya daga cikin bukatun masu zanga-zangar adawa da manufofin gwamnati mai ci shi ne a dawo da tallafin man fetur wanda shugaban ƙasa Bola Tinubu ya tuge tun ranar farko.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Daily Trust ta ce a jawabin da ya yi ranar Lahadi, Shugaba Bola Tinubu ya kore yiwuwar mayar da tallafin, yana mai cewa cire shi yana da zafi amma ya zama dole.

Matsalar dawo da tallafin man fetur

Da yake jawabi a Sunrise Daily, shirin safe na Channels tv ranar Laraba, Issa-Onilu ya shawarci 'yan Najeriya da su tsara dabarun rayuwa bayan cire tallafin mai.

Daraktan NOA ya ce:

"Duk wanda ka ji ya bukaci a dawo da tallafin man fetur, ya yi haka ne don son ransa amma ba wai don amfanin tattalin arziki ba.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: An kama mutumin da ke ɗinka tutocin ƙasar Rasha a jihar Kano

"Saboda haka idan kuna bukatar a dawo da shi sai kun gamsar da mu cewa hakan zai magance talauci. Ba zai warkar da mutane ba sai dai ya kara jefa su a bakin talauci."

Daraktan NOA ya ƙara da cewa babbar matsalar da ake samu tsakanin mabiya da shugabanni ta samo asali ne daga rashin cika alƙawurra na tsawon shekaru.

Hafsoshin tsaron ECOWAS sun gana a Abuja

Kuna da labarin hafsoshin tsaro na ƙasashen ƙungiyar ECOWAS sun gana a birnin tarayya Abuja karkashin jagorancin Janar Christopher Musa.

Taron wanda ya gudana a hedkwatar tsaro ta kasa ya samu halartar duka hafsoshin tsaron kasashen yammacin Afirka ban da na ƙasashe uku.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262