Kasar Rasha Ta Yi Magana Kan Masu Zanga Zangar da ke Ɗaga Tutocinta a Najeriya

Kasar Rasha Ta Yi Magana Kan Masu Zanga Zangar da ke Ɗaga Tutocinta a Najeriya

  • Ƙasar Rasha ta musanta raɗe-raɗin cewa tana da hannu a ɗaga tutocin da matasa masu zanga-zanga ke yi a Najeriya
  • Ofishin jakadancin Rasha a Najeriya ya ce gwamnatin Shugaba Putin ba ta sa baki a harkokin cikin gida na kowace ƙasa a duniya
  • Wannan na zuwa ne a lokacin da masu zanga-zangar adawa da manufofin gwamnatin Bola Tinubu suka fara ɗaga tutar Rasha musamman a Arewa

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Ƙasar Rasha ta musanta cewa tana da hannu a ɗinkawa da ɗaga tutocin ƙasar da wasu masu zanga-zanga ke yi a Arewacin Najeriya.

Ofishin jakadancin Rasha a Najeriya ne ya bayyana haka, ya ce ko kaɗan ba su da hannu a tawagar matasan da aka ga suna ɗaga tutocin Rasha yayin da suka fito zanga-zanga.

Kara karanta wannan

Babban hafsan tsaro ya fadi laifin masu daga tutar Rasha, ya gargadi 'yan zanga zanga

Masu zanga zanga da Tinubu.
Rasha ta jaddada cewa ba ta tsoma baki a harkonin ciki gida na kowace ƙasa a duniya Hoto: @KawuGarba, @OfficialABAT
Asali: Twitter

Daily Trust ta tattaro cewa masu zanga-zanga a wasu jihohi sun fito kan tituna ɗauke da tutocin kasar Rasha kuma suna rera taken ƙasar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ana dai zargin Rasha, ƙasa mai karfin fada a ji a duniya da hannu a rikice-rikicen siyasa na baya-bayan nan a wasu kasashen yammacin Afirka da suka hada da Mali, Burkina Faso, da Nijar.

Zanga-zanga: A karshe Rasha ta magantu

A wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin, ofishin jakadancin ya jaddada cewa Rasha ba ta tsoma baki cikin harkokin wasu kasashe ciki har da Najeriya.

"Mun lura da wasu rahotannin da kafafen yada labarai na Najeriya ke yadawa da bidiyo da hotuna da ke nuna masu zanga-zanga dauke da tutocin Rasha suna rera taken shugaban Rasha Vladimir Putin.
"Gwamnatin Rasha da jami'anta ba su da hannu ko kaɗan a lamarin kuma ba ta da alaƙa da su. Kamar kowane lokaci muna kara jaddada cewa Rasha ba ta tsoma baki a harkokin ƙasashe ciki har da Najeriya."

Kara karanta wannan

Zanga zanga: An kama mutumin da ke ɗinka tutocin ƙasar Rasha a jihar Kano

Sanarwar ta ƙara da cewa Rasha na mutunta tsarin demokuraɗyyar Najeriya kuma tana Allah wadai da duk wani abu da zai haifar da tashin-tashina a ƙasar nan, rahoton The Nation.

Ƴan sanda sun kama telan tutocin Rasha

A wani rahoton kuma jami'an tsaro sun kama wani tela mai suna Ahmed bisa zarginsa da yaɗa tutocin ƙasar Rasha a jihar Kano a lokacin zanga-zanga.

Rahotanni sun nuna matasa sun fara ɗaga tutocin ƙasar ketaren ne a makon da ya wuce, amma lamarin ya ƙara yaɗuwa a ranar Litinin.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262