Gwamna Abba Ya Ɗauki Mataki Kan Masu Zanga Zanga a Kano, Ya Aika Masu Goron Gayyata

Gwamna Abba Ya Ɗauki Mataki Kan Masu Zanga Zanga a Kano, Ya Aika Masu Goron Gayyata

  • Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya gana da malamai, sarakuna da ƴan kasuwa a gidan gwamnati kan zanga-zangar da za a fara
  • Gwamma Abba ya ce gwamnatinsa ba za ta lamunci duk wani abin da zai tada hankula ba a lokacin zanga zanga
  • Ya kuma gayyaci masu shirin yin zanga-zangar domin su zo gidan gwamnatin Kano su tattauna kan kokensu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kano - Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya ce gwamnati ba za ta lamunci wani yunkuri ba zai kawo tashin hankali ba a zanga-zangar da za a yi gobe Alhamis.

Abba Kabir ya faɗi haka ne a lokacin da yake jawabi ga ’yan kasuwa, sarakunan gargajiya, da malaman addini a gidan gwamnati da ke Kano yau Laraba.

Kara karanta wannan

Gwamnan Arewa ya fito fili ya goyi bayan zanga zanga, ya caccaki 'yan sanda

Gwamna Abba Kabir Yusuf.
Gwamna Abba Kabir ya gayyaci masu shirin zanga-zanga a Kano Hoto: Abba Kabir Yusuf
Asali: Facebook

Gwamna ya jaddada cewa zanga-zanga ba za ta kai mutane ko'in ba, bisahaƙa ya ja kunnen matasa su guje wa tada zaune tsaye, kamar yadda Daily Trust ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya kuma ƙara da rokon masu shirin yin amfani da ‘yancinsu na fitowa zanga-zanga da su kaucewa duk wani hali da ɓata gari za su yi amfani da shi wajen tayar da tarzoma.

Gwamnan Abba ya gayyaci masu zanga-zanga

"Mun samu sahihan bayanan sirri cewa wasu daiɗaikun mutane sun ɗauko hayar ƴan daba domin tada fitina a jihar Kano. Ina tabbatar muku da cewa gwamnati ba za ta lamunci haka ba.
"A maimakon haka, ina mika goron gayyata ga masu son gudanar da zanga-zanga da su zo gidan gwamnati, inda zan ji dadin sauraren koke-kokensu, sannan mu tattauna da su."

- Abba Kabir Yusuf.

Gwamna ya ambaci wasu tsare-tsaren da gwamnatinsa ta kawo na inganta rayuwar al'umma da kuma tsamo su daga halin wahalar da ake ciki.

Kara karanta wannan

Ana saura kwana 1, gwamnatin Tinubu ta aike da muhimmin saƙo kan zanga zanga

Gwamnatin Tinubu ya roki ƴan Najeriya

A wani rahoton kuma Sakataren gwamnatin tarayya, George Akume ya roƙi ƴan Najeriya sun gujewa zanga zangar da aka shirya yi a watan Agusta.

Sanata Akume ya tabbatar wa al'umma cewa wannan wahalar da ake ciki ba za ta dawwama ba, nan gaba kaɗan za a ji daɗi.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262