An Maka Bankin CBN Kara Gaban Kotu Kan Manyan Laifuffuka 3, Bayanai Sun Fito

An Maka Bankin CBN Kara Gaban Kotu Kan Manyan Laifuffuka 3, Bayanai Sun Fito

  • Ƙungiyar SERAP ta ce ta maka babban bankin Najeriya (CBN) a gaban kotu bisa zargin ɓatan N100bn na yagaggun kuɗi
  • SERAP ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi, 28 ga watan Yuli, ta hannun mataimakin daraktan ta, Kolawole Oluwadare
  • A cewar ƙungiyar, ta shigar da ƙarar ne a gaban babban kotun tarayya da ke birnin Legas a makon da ya gabata

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Opebi, Ikeja - Ƙungiyar SERAP ta maka babban bankin Najeriya (CBN) ƙara a bisa zargin gaza yin bayanin inda sama da N100bn na yagaggun kuɗi suka yi.

SERAP ta ce tana kuma ɗaukar matakin shari’a a kan CBN saboda N12bn da aka warewa ofisoshin babban bankin a Abeokuta, jihar Ogun, da kuma Dutse a jihar Jigawa.

Kara karanta wannan

Ana harin zanga zanga, gwamnatin tarayya ta dauki muhimmin mataki

SERAP ta shigar da CBN kara
Kungiyar SERAP ta shigar da CBN kara gaban kotu Hoto: Bloomberg
Asali: Getty Images

TABLE OF CONTENTS

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta sanya a shafinta na X a ranar Lahadi, 28 ga watan Yulin 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

CBN ya saɓa doka - SERAP

Wani dalili kuma da ya sa ƙungiyar SERAP ta kai ƙarar CBN a gaban kotu shi ne bashin N3bn da aka ba jihohin Anambra da Enugu.

An shigar da ƙarar mai lamba FHC/L/MSC/441/2024 a makon da ya gabata a babbar kotun tarayya da ke Legas.

A halin yanzu dai, ba a sanya ranar da za a fara sauraron ƙarar ba.

Zarge-zarge 3 da SERAP ke yiwa CBN

  1. Rashin bayyana inda sama da N100bn na yagaggun kuɗi da waɗanda suka lalace suke.
  2. N12bn da aka ware wa ofisoshin CBN a Abeokuta da Dutse
  3. Bashin N3bn da aka ba jihohin Anambra da Enugu

Kara karanta wannan

Gwamna ya yi watsi da batun zanga zanga, ya fadi matakan da ya dauka

Karanta wasu labaran kan CBN

SERAP za ta yi ƙarar gwamnoni

A wani labarin kuma, kun ji cewa ƙungiyar da ke rajin bin diddigin ayyukan tattali ta SERAP, ta gargadi gwamnonin jihohi 36 na Najeriya da ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike.

SERAP ta sanar da bukaci gwamnonin kasar da ministan Abuja da su hanzarta mayar da kudaden kananan hukumomi da suka kalmashe

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng