Zanga Zanga: Kungiyar Matasan Najeriya ta Tura Sako Zuwa ga Rassanta 104

Zanga Zanga: Kungiyar Matasan Najeriya ta Tura Sako Zuwa ga Rassanta 104

  • Kungiyar matasan Najeriya ta National Youth Council of Nigeria (NYCN) bayyana damuwa dangane da halin da 'yan kasa su ka tsinci kansu na kunci
  • Shugaban kungiyar na kasa, Sukubo Sara-Igbe Sukubo ne ya bayyana damuwarsu bayan taron gaggawa da su ka gudanar ranar Alhamis
  • Ya umarci rassanta 104 da ke jihohin kasar nan 36 da su jira umarni na gaba wanda za a sanar a karshen watan Yuli

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT, Abuja - Kungiyar matasan kasar nan ta National Youth Council of Nigeria (NYCN) ta bayyana rashin jin dadi a kan yadda 'yan kasar nan ke cikin wahala yayin da ake shirin zanga-zanga.

Kara karanta wannan

Hedkwatar tsaro ta jero mutanen da ake shirin kai wa hari a lokacin zanga zanga

Wannan na zuwa a lokacin da kasar ta kasa zaune ta kasa tsaye saboda batun zanga-zanga da 'yan kasa su ka ce sai sun gudanar a watan Agusta mai kamawa.

Amb Sukubo Saraigbe Sukubo
Kungiyar matasa za ta fadi matsayarta a kan zanga-zanga Horo: Amb Sukubo Saraigbe Sukubo
Source: Facebook

Jaridar Daily Trust ta wallafa cewa Sukubo Sara Igbe Sukubo ya gana da sauran shugabannin kungiyoyin matasa da jiha a kan batun zanga-zanga da sauran natsalolin da su ka shafi kasa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Zanga-zanga: Matasa za su bayyana matsayarsu

Kungiyar matasa ta NYCN ta bayyana cewa za ta fadi matsayarta a kan tafiya a kan zanga-zangar gama gari a karshen watan Yuli, Leadership ta wallafa.

Shugaban kungiyar, Sukubo Sara Igbe ne ya bayyana haka, inda ya ce za su fitar da matsayarsu a taron da za su gudanar ranar Laraba 31 Yuli, 2024.

Ya ce taronsu na yau Alhamis ya tattauna da shugabannin kungiyar a jihohi, inda aka zanta a kan tsadar rayuwa da bukatar daukar matakin da ya kamata.

An shawarci matasa a kan zanga-zanga

A baya mun ruwaito cewa tsohon dan takarar shugaban kasa a shekarar 2019, Faduri Oluwadare Joseph ya goyi bayan zanga-zanga da ake shirin yi daga farkon Agusta zuwa 10 Agusta, 2024.

Kara karanta wannan

"Ba mu san dalilinku ba:" Gwamnonin APC sun tura sako ga matasa kan zanga-zanga

Tsohon dan takarar shugaban kasar ya bayyana cewa amma dole sai matasa sun sa ido sosai saboda gujewa kutsen bata-gari da ka iya tayar da tarzoma da ka iya jawo asarar rayuka.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng