Assha: Zaune Bata Kare Ba a Najeriya, Wutar Lantarki Ta Sake Baci a Duk Fadin Kasa

Assha: Zaune Bata Kare Ba a Najeriya, Wutar Lantarki Ta Sake Baci a Duk Fadin Kasa

  • Tushen wutar lantarkin Najeriya ya sake rushewa bayan da aka samu aukuwar hakan a lokuta mabambanta
  • Wannan ne karo na hudu da Najeriya ke fuskantar lalacewar wuta tare da jefa ‘yan kasa a duhu a shekarar nan
  • A tattaunawar Legit Hausa da wani dan kasuwa a Abuja, ya ce rashin wuta na taba kasuwancinsu ainun

Salisu Ibrahim ne babban editan sashen Hausa na Legit. Kwararren marubucin fasaha, harkar kudi da al'amuran yau da kullum ne, yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru takwas

Najeriya - An sake samun rushewar tushen karafan rarraba wutar lantarki na Najeriya, inda yanzu kasar ke samar da 0.80MW na wutar lantarki.

Binciken da aka yi ya nuna cewa, wutar ta fara raguwa ne da kimanin karfe 2 na rana zuwa 2,797.16MW daga akalla 3,417.99MW da misalign karfe 1 na rana.

Kara karanta wannan

Kano: Fusatattun matasa sun fatattaki wakilin Sanusi II daga Karaye bayan cire masu Sarki

Wutar ta kara raguwa zuwa 1,020.08MW da misalin karfe 3 na rana kafin ta karasa raguwa sosai zuwa 0.80MW da misalin karfe 4 na yamma.

Wutar Najeriya ta sake baci
An samu matsala, wutar Najeriya ta sake baci | Hoto: TCN
Asali: Getty Images

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Adadin wutar lantarkin da ake samu a Najeriya yanzu

Daily Trust ta ruwaito cewa, sashen samar da wutar lantarki na Trans-Amadi Power plant ne ya samar da wannan 0.80MW da aka samu.

Wannan shine karo na hudu da turken rarraba wutar lantarkin Najeriya ya rushe a cikin shekarar 2024 da ake ciki yanzu.

Ta tabbata wuta ta lalace a Najeriya

Da yake tabbatar da rushewar, Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Enugu (EEDC) ya ce lamarin ya faru ne kimanin karfe 3:09 na yamma.

Wata sanarwar da aka rabawa manema labarai da shugaban hulda da jama'a na kamfanin, Emeka Ezeh, ya sa wa hannu ta bayyana cewa lamarin ya haifar gimtsewar wutar lantarki a yankunan da hakan ya shafa.

Kara karanta wannan

Majalisa za ta binciki kwangilar aikin Mambila, za a dauko aikin wutar tun daga 1999

An kara kudin wuta a Najeriya, NLC ta tura bukata

A bangare guda, kungiyar kwadagon Najeriya ta yi kira ga gwamnati da a gaggauta janye karin kudin wutar lantarki da kamfanonin DISCOs suka yi ga abokan huldar na tsarin “Band A”.

Daga ranar 1 ga Yuli, 2024, masu shan wutar lantarki a karkashin tsarin "Band A" za su biya N209.5/KWh maimakon N206.80/KWh da suke biya a baya.

A cikin wata sanarwa da ya aike wa jaridar The Punch, shugaban kungiyar NLC, Kwamared Joe Ajaero, ya bayyana karin a matsayin "tsantsar rashin adalci da girman kai".

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.