ASUU Ta Fara Shirin Shiga Yajin Aiki, Ta Gargadi Gwamnatin Tarayya

ASUU Ta Fara Shirin Shiga Yajin Aiki, Ta Gargadi Gwamnatin Tarayya

  • Ƙungiyar malaman jami'a ta Najeriya (ASUU) ta nemi gwamnatin tarayya da ta cika mata buƙatun da take nema a wajenta
  • Ƙungiyar ASUU ta yi barazanar cewa za ta shiga yajin aiki nan da makonni biyu idan har ba a cika mata buƙatun ba
  • ASUU ta koka kan yadda ba a sauyawa malaman jami'a albashinsu ba a cikin shekara 15 da suka gabata a ƙasar nan

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Abia - Ƙungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta biya buƙatunta na inganta walwalar malaman jami'a.

ASUU ta yi gargaɗin cewa rashin cika waɗannan buƙatun ka iya sanyawa ta tsunduma cikin yajin aiki nan da makonni biyu.

Kara karanta wannan

Majalisa ta fadi matakin dauka idan Tinubu ya bukaci a siyo masa jirgin sama

ASUU ta gargadi gwamnatin tarayya
ASUU ta gargadi gwamnatin tarayya kan shirin shiga yajin aiki Hoto: @asuunews, @PBATMediaCentre
Asali: Twitter

Shugabar ASUU ta shiyyar Calabar, Misis Happiness Uduk ta bayyana hakan a yayin ganawa da manema labarai a jami'ar jihar Abia (ABSU) a ranar Juma'a, cewar rahoton jaridar Tribune.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Me ASUU ta ce kan shiga yajin aiki?

Ta nuna cewa cika waɗannan buƙatu na da matuƙar muhimmanci domin hana afkawa yajin aikin gama-gari a faɗin ƙasar nan.

Happiness Uduk ta nuna gazawar gwamnatin tarayya wajen cika yarjejeniyar da ta cimmawa da ƙungiyar a shekarar 2009, rahoton jaridar PM News ya tabbatar.

Ta ce hakan ya sanya albashin malaman jami'a bai sauya ba cikin shekara 15 da suka gabata.

"Albashin mambobin ASUU bai sauya ba a cikin shekara 15. Muna kira ga gwamnati da ta kammala tattaunawar da aka fara shekara 13 da suka gabata tare da yin la'akari da halin da tattalin arziƙin ƙasar nan yake ciki a yanzu."

Kara karanta wannan

ASUU ta tsorata Gwamnatin Bola Tinubu, an fara zaman tattaunawa a Abuja

- Misis Happiness Uduk

Ta buƙaci tawagar tattaunawar su gaggauta samar da mafita kan kuɗaɗen ceto jami'o'in gwamnati, biyan kuɗaɗen alawus, albashin da aka riƙe, yawan haraji da muzgunawa mambobin ASUU.

Batun yajin aikin ASUU

A wani labarin kuma, shugaban ƙungiyar malaman jami'o'i (ASUU), Farfesa Emmanuel Osodoke ya ce ƙungiyar na duba yiwuwar janyewa daga kudirin shiga yajin aikin da suka yi niyya a baya.

Farfesa Osodoke ya ce sun fara duba batun ne bayan ganawarsu da jami'an gwamnatin tarayya karkashin jagorancin ministocin Ilimi, Farfesa Tahir Mamman da Dakta Tanko Sununu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng

Online view pixel