'Yan Bindiga Sun Yi Yunƙurin Takaita Babban Limamin Musulmi a jihar Kaduna

'Yan Bindiga Sun Yi Yunƙurin Takaita Babban Limamin Musulmi a jihar Kaduna

  • Ƴan bindiga sun kai hari kauyen Gidan-Makera a ƙaramar hukumar Kagarko da ke jihar Kaduna, sun tafi da shanun babban limamin garin
  • Mazauna yankin sun bayyana cewa wasu ƴan banga sun yi nasarar kwato shanun bayan sun bi bayansu ranar Talata
  • Shu'aibu Ahmadu, wani mazaunin yankin ya ce limamin, Malam Ibrahim Zubairu ba ya gida lokacin da lamarin ya auku ranar Talata da yamma

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kaduna - ‘Yan bindiga sun sace shanu 73 na babban limamin Gidan-Makeri, Malam Ibrahim Zubairu, a karamar hukumar Kagarko da ke jihar Kaduna.

Wani mazaunin kauyen Kuchimi da ke makwabtaka da Gidan-Makeri, Shuaibu Ahmadu ya ce lamarin ya faru ne a ranar Talata da misalin karfe 5:33 na yamma.

Kara karanta wannan

Ruwa ya cinye wasu dalibai a hanyarsu ta dawo wa daga jarrabawa a Kaduna

Taswirar jihar Kaduna
Yan bindiga sun yi yunkurin sace shanun babban limami a jihar Kaduna
Asali: Original

Harin 'yan bindiga a kauyen Kaduna

Ya ce maharan ɗauke da miyagun bindigu kuma da adadi mai yawa sun kutsa kai yankin, kana suka yi yunƙurin sace shanun Malamin Addinin Musuluncin, Daily Trust ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mutumin ya ƙara da cewa daga zuwan ƴan bindigar suka wuce kai tsaye zuwa wurin da aka killace shanun a bayan garin, suka tattara su suka tafi.

Shu'aibu ya ce maharan sun riƙa harbe-harbe a iska domin tsorata mazauna garin kada su biyo bayansu a lokacin da suka kora shanun zuwa cikin jeji.

A cewarsa liman Malam Ibrahim ya yi tafiya zuwa Kagarko a lokacin da ƴan ta'addan suka kawo farmakin.

Yan banga sun kwato shanun liman

Bayan samun labarin abin da ya faru, ƴan banga daga kauyen Kachimi mai maƙwaftaka da Gdan-Makeri, suka bi sawun ƴan bindigar.

Kara karanta wannan

An shiga rudani, 'yan ta'adda sun lafta harajin wata wata a kan mazauna Binuwai

“Limamin yana Kagarko a lokacin amma da ikon Allah daga baya ’yan banga daga kauyen Kuchimi da ke makwabtaka suka kwato shanun daga hannun ƴan fashin dajin."

An tattaro cewa shanun sun yi gardama wajen tsallaka kogin Gurara, lamarin da ya tilasta wa ‘yan bindigar tserewa suka barsu a nan kafin isowar ‘yan banga.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, ASP Hassan Mansur, bai fitar da wata sanarwa a hukumance kan harin ba har kawo yanzu.

Matar aure ta kashe mijinta a Yobe

A wani rahoton, ƴan sanda sun kama wata matar aure Zainab Isa bisa zargin daɓawa mijinta wuta har lahira a Abbari da ke cikin Damaturu a jihar Yobe

Mai magana da yawun ƴan sandan jihar DSP Dungus Abdulkareem ya ce lamarin ya faru ne a lokacin da saɓani ya shiga tsakanin ma'auratan.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel