'Yan Sandan Kaduna Sun Kama Mutane 3 Kan Zargin Satar Kebura

'Yan Sandan Kaduna Sun Kama Mutane 3 Kan Zargin Satar Kebura

Kaduna - Rundunar yan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wasu mutane uku bisa zargin satar wayar wuta ta alminiyo a garin Saminaka da ke karamar hukumar Lere ta jihar.

Mai magana da yawun rundunar, ASP Mansir Hassan, shi ya bayyana haka ranar Lahadi a Kaduna.

An kama wasu matasa 3 kan zargin satar kebura a Kaduna
'Yan Sandan Kaduna Sun Kama Mutane 3 Kan Zargin Satar Kebura.
Asali: Facebook

Hassan ya ce da misalin karfe 4:00 na asuba ranar Lahadi, rundunar ta samu rahoton satar wayar wuta a wata karamar unguwa da ke titin Kafanchan, Garin Saminaka, cewa an ga wasu da ba a san ko su waye da wayar wuta.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Tawagar sintirinmu sun dira unguwar, kuma sun kama wanda ake zargi su uku da suka fito daga Unguwar Bawa", in ji shi.

Kara karanta wannan

NDLEA ta kama dillali da ke sayarwa 'yan bindiga kwayoyi a Zamfara da Kebbi

Hassan ya ce an kama wanda ake zargin da wayar wuta ta alminiyo da adduna lokacin da aka kama su.

A cewarsa, wanda ake zargin sun amsa laifin yanko wayar wuta daga turakun wuta a titin Saminaka-Kafanchan.

Hassan, ya bayyana cewa tuni aka sanar da lamarin ga kamfanin rarraba wuta na Kaduna, ya ce har yanzu ana ci gaba da bincike.

Ya ce za a tura wanda ake zargin kotu da zarar an kammala bincike

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164