Abbas Ya Kafa Kwamiti a Majalisa, Za Su Gana Da Tinubu Kan Shirin Shiga Yajin Aikin Likitoci

Abbas Ya Kafa Kwamiti a Majalisa, Za Su Gana Da Tinubu Kan Shirin Shiga Yajin Aikin Likitoci

  • Majalisar wakilai na yin duk wacca za su iya don dakile shirin shiga yajin aikin da kungiyar likitocin Najeriya ke yi
  • Daga cikin kokarin da yake yi na hana yunkurin, kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, na shirin ganawa da shugaban kasa, Asiwaju Bola Tinubu
  • A cewar Abbas wannan ganawar na da matukar muhimmanci domin zai magance da samo maslaha ga yajin aikin likitocin

FCT, Abuja - Kakakin majalisar wakilai, Honourable Tajudeen Abbas, na shirin ganawa da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

Jaridar Punch ta rahoto cewa ganawar da za a yi tsakanin Abbas da shugaban kasar na daga cikin kokarin da ake yi na dakile shirin da kungiyar likitocin Najeriya (NARD) ke yi na shiga yajin aiki.

Kakakin majalisa, Tajudeen Abbas zai gana da shugaban kasa Bola Tinubu
Abbas Ya Kafa Kwamiti a Majalisa, Za Su Gana Da Tinubu Kan Shirin Shiga Yajin Aikin Likitoci Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, House of Representatives, Federal Republic of Nigeria
Asali: Facebook

Batutuwan da za su tattauna

Abbas ya kuma bayyana cewa zai gana da Tinubu ne domin sanar da shi batutuwan da kungiyar NARD ta gabatar tare da kira ga shugaban kasa kan yadda zai warware su.

Kara karanta wannan

A Kurarren Lokaci, Tinubu Ya Cire Mutum 4 a Jerin Wadanda Za A Ba Kujerar Minista

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Hakan na zuwa ne yan awanni bayan kakakin majalisar ya bukaci fusatattun likitocin da su janye yajin aikin da suke shirin shiga da kuma ba majalisar damar yin tunani a kan al’amuran da ke gabansu, rahoton Nigerian Tribune.

A yayin ganawa da shugabancin NARD na kasa a ofishinsa da ke Abuja, a ranar Litinin, Hon. Abbas ya kuma sanar da kafa wani kwamitin wucin gadi karkashin jagorancin shugaban majalisa, Farfesa Julius Ihonvbere.

Kwamiin zai gana da dukkan masu ruwa da tsaki domin magance lamuran, jaridar Leadership ta rahoto.

Fasto ya bukaci APC da ta zabi Al-makura a matsayin shugaban jam'iyyar na kasa maimakon Ganduje

A wani labari na daban, Primate Elijah Ayodele, shugaban cocin INRI Evangelical Spiritual ya ce mutumin da ya fi dacewa da shugabancin jam'iyyar All Progressive Congress (APC) shine tsohon gwamnan jihar Nasarawa, Sanata Tanko Al-Makura.

Malamin addinin wanda ya yi suna wajen yin hasashe ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa dauke da sa hannun kakakinsa, Osho Oluwatosin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng