29 Ga Watan Mayu: UK, Iran, Qatar Da Wasu Kasashe 40 Da Buhari Ya Ziyarta a Matsayin Shugaban Kasar Najeriya

29 Ga Watan Mayu: UK, Iran, Qatar Da Wasu Kasashe 40 Da Buhari Ya Ziyarta a Matsayin Shugaban Kasar Najeriya

Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kammala wa’adin mulkinsa a matsayin jagora na daya a Najeriya cikin kasa da kwanaki 35 masu zuwa yayin da ranar 29 ga watan Maris ke kara gabatowa.

A matsayinsa na shugaban kasar Najeriya, an sha caccakar Buhari saboda kasancewarsa shugaban kasa mafi yawan tafiye-tafiye da aka taba samu a Afrika ta yamma.

A cewar jaridar The Punch, Buhari ya ziyarci kasashen duniya 40 a matsayin shugaban kasa kuma ya yi tafiye-tafiyen kasashen waje 90 a shekaru 8 a Najeriya.

Shugaban kasa Buhari ya ziyarci kasashe da dama
29 Ga Watan Mayu: UK, Iran, Qatar Da Wasu Kasashe 40 Da Buhari Ya Ziyarta a Matsayin Shugaban Kasar Najeriya Hoto: Femi Adesina
Source: Facebook

Da ake nazarin shekaru 8 da ya yi a matsayin shugaban kasa, Buhari ya ziyarci akalla kasashe 43 a fadin duniya.

Kasashen da Buhari ya ziyarta sun kasance a fadin kasashen duniya kuma yawanci ziyar aiki, na ganin likita da kuma sauke farali ne.

Kara karanta wannan

Waiwaye Ga Mulkin Buhari: Manyan Alkawura 3 Da Buhari Ya Dauka, Amma Ya Gaza Cika Wa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Legit.ng ta tattaro rukunin sunayen wadannan kasashe da ya ziyarta da kuma yadda shugaban kasar ya dungi ziyartansu yayin da yake shugabancin Najeriya.

Kasashen da Buhari ya fi ziyarta

S/N

Kasashe

1

Amurka

2

Birtaniya

3

Saudiyya

4

Habasha

5

Faransa

Kasashen da Buhari ya ziyarta tsakanin sau 3-6

S/N

Kasashe

1

Afrika ta kudu (3x)

2

Hadaddiyar daular Larabawa (3x)

3

Ghana (3x)

4

Nijar (3x)

5

Senegal (4x)

Kasashen da Shugaba Buhari ya ziyarta akalla sau 2

1

Jordan

2

Sin

3

Jamus

4

Gambiya

5

Benin

6

Kenya

7

Equatorial Guinea

8

Côte d'Ivoire

9

Qatar

10

Chadi

11

Morocco

Ga jerin sauran kasashe 22 da Buhari ya ziyarta a matsayin shugaban kasar Najeriya a kasa

1

Belgium

2

Burkina Faso

3

Cameroon

4

Egypt

5

Guinea-Bissau

6

India

7

Iran

8

Japan

9

Liberia

10

Mali

11

Malta

12

Mauritania

13

Netherlands

14

Rasha

15

Rwanda

16

Poland

17

Portugal

18

Koriya ta Kudu

19

Spain

20

Sudan

21

Togo

22

Turkiyya

Kara karanta wannan

Arewacin Najeriya Zai Samu Gas da Lantarki, An Yi 70% na Aikin AKK Inji NNPCL

Rikicin Sudan: Peter Obi ya aika muhimmin sako ga Buhari

A wani labarin dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party, Peter Obi ya bukaci shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya yi duk mai yiwuwa wajen kwashe yan Najeriya da suka makale a Sudan cewa hakki ne da ya rataya a wuyansa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng