Kungiyar Musulmai Ta MURIC Ta Fusata, Shugabar Makaranta Ta Cire Hijabin Dalibar Sakandare

Kungiyar Musulmai Ta MURIC Ta Fusata, Shugabar Makaranta Ta Cire Hijabin Dalibar Sakandare

  • Kungiyar kare hakkin Musulmai ta MURIC ta fusata bisa samun labarin yadda aka ci zarafin wata dalibar sakandare
  • Shugabar makaranta a jihar Legas ta cire hijabin wata dalibar sakandare, lamarin da ya fusata kungiyar ta Muslunci
  • Ana ci gaba da samun cece-kuce kan batun sanya hijabi a jihohin Kudancin Najeriya, lamarin da ke kara daukar zafi

Jihar Legas - Kungiyar kare hakkin Musulmai (MURIC) ta bukaci ma’aikatar ilimi ta jihar Legas da ta binciki wata shugabar makarantar sakandaren Eletu Odibo da sauran malamai a makarantar bisa zargin cirewa wata daliba hijabi.

Shugaban kungiyar, farfesa Ishaq Akintola ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis 22 ga watan Disamba a cikin wata sanarwa da ya fitar, Daily Trust ta ruwaito.

Sanarwar ta bayyana, ana zargin shugabar makarantar, Mrs Christiana Sofuye da ba da umarnin a cire hijabin wata daliba mai suna Mujeebat AbdulQadri ‘yar a

Kara karanta wannan

Gwamna Ya Karawa Ma’aikatan Jiha Albashi da 10%, Ya Rabawa Kowa Goron Kirismeti

Malamar makaranta ta jawo rikici bayan cire hibajin daliba
Kungiyar Musulmai Ta MURIC Ta Fusata, Shugabar Makaranta Ta Cire Hijabin Dalibar Sakandare | Hoto: muricnigeria.com
Asali: UGC

i biyu na karamar sakandare a bainar jama’a a makarantar.

An ci zarafin daliba, hakan ya saba dokar Legas da majalisar dinkin duniya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

MURIC ta ce, wannan aiki ya saba da doka kuma hakan zai iya tunzura al’umma matular ya ci gaba da faruwa.

Hakazalika, Akintola ya bayyana cewa, kotun koli a jihar Legas ta yi hukunci kan halascin sanya hibaji a makarantun jihar a ranar 17 ga watan Yulin 2022, kamar yadda kungiyar ta fada cikin wata sanarwa.

A bangare guda, ya ce cire ma dalibar hijabi daidai yake da cin zarafin yara da kuma take hakkin addini kamar yadda yanzo a bayanan majalisar dinikin duniya.

Hakazalika, ya ce ya yi mamakin yadda shugabar makarantar ta yi biris da umarnin gwamnatin jihar Legas na ranar 6 ga watan Disamba na ba dalibai mata damar sanya hijabi a makarantun gwamnati a jihar.

Kara karanta wannan

Jarumta: Yadda budurwa ta lallasa 'yan bindiga masu AK47, ta ceto mutum 3 a hannunsu

Rikicin Hijab a Kwara: Iyalan wanda aka kashe sun nemi a biya su diyyar N113m

Rikicin sanya hijabi a jihar Kwara ya kai ga mutuwar mutane, iyalan wadanda aka kashe sun bayyana neman diyya daga gwamnati.

A jihar ta Kwara, an sha kai ruwa rana kan haramtawa dalibai mata musulmai sanya hijabi a makarantun gwamnati.

Hakan na ci gaba da daukar yanayi mara dadi a yankunan Kudancin kasar nan, gwamnati da hukumomi na daukar mataki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.

Tags: