Yan Bindiga Sun Kashe Babban Limami Da Wasu Mutum 2 a Sokoto

Yan Bindiga Sun Kashe Babban Limami Da Wasu Mutum 2 a Sokoto

  • Tsagerun yan bindiga sun farmaki al'ummar yankin Sabon Birni a jihar Sokoto inda suka kashe wani babban limami a Gangara
  • Yan bindiga sun kuma farma wasu manoma yayin da suke tsaka da aiki a gonakinsu a kauyen Dunkawa, sun kuma kashe mutum biyu da awon gaba da wasu
  • Har ila yau masu fashi da makami sun hari motocin fashinja a titin Sabon Birni-Isa yayin da suke hanyar zuwa cin kasuwa, sun lale masu kudade da abubuwan amfani

Sokoto - Rahotanni daga Daily Trust sun nuna cewa yan bindiga sun kashe mutane uku ciki harda babban limamin Gangara a karamar hukumar Sabon Birni da ke jihar Sokoto.

An tattaro cewa an kashe limamin wanda ake kira da Liman Na-Kimba a ranar Laraba yayin da yake dawowa daga Sokoto inda ya je karbar kudin fansho dinsa.

Kara karanta wannan

Luguden NAF Ya Halaka Manyan Yan Bindiga 3 da Ake Nema da Mayankansu a Jihohin Arewa

Yan bindiga
Yan Bindiga Sun Kashe Babban Limami Da Wasu Mutum 2 a Sokoto Hoto: Premium Times
Asali: UGC

A cewar wasu shaidu, motocinsu ya fada komadar yan bindiga a hanyar kauye Adamawa sai makasansu suka bude masu wuta.

Majiya ta ce:

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

"Daya daga cikin harsasan ya samu limamin ya kuma kashe shi."

Yan bindiga sun halaka manoma biyu a kauyen Dunkawa

A halin da ake ciki, yan bindiga sun kuma kashe wasu manoma biyu a kauyen Dunkawa karkashin yankin Gatawa duk a karamar hukumar ta Sabon Birni kwanaki hudu da suka shige.

Yan bindigar sun kuma yi garkuwa da wasu manoma shida yayin da suke aiki a gonakinsu.

Shugaban kungiyar yan banga a Sabon Birni, Musa Muhammad, wanda ya tabbatar da lamarin ya ce an kashe manoman ne a gonakinsu kwanaki hudu da suka shige.

Ya ce:

"Sun same su suna aiki a gonakinsu, sai suka kashe biyu sannan suka sace wasu shida."

Kara karanta wannan

Gwamna Zulum Ya Gwangwaje Jama’ar Ngala da N255m, Kayan Abinci da Sutturu

A cewarsa an binne duk mamatan daidai da koyarwar addinin Musulunci. Ya koka cewa yan bindigar sun kawo dabbobi don lalata gonaki a garuruwan.

Mahara sun yiwa fasinjoji fashi a titin Sabon Birni-Isa

A wani ci gaban, yan fashi sun toshe Sabon Birni-Isa a ranar Alhamis sannan suka yiwa fasinjoji fashin kudade da sauran kayayyakinsu.

Muhammad ya fadama jaridar cewa mutanen da abun ya ritsa da su suna a hanyarsu ta zuwa kasuwar mako da ke ci a karamar hukunar Shinkafi ta jihar Zamfara daga Sabon Birni.

Ya bayyana cewa, lamarin ya afki ne a hanyar kauyikan Makwaruwa -Turba da misalin karfe 8:00am.

Ya ce yan bindigar sun shafe fiye da awa biyu suna fashi a hanyar amma babu wani rahoto na kisa ko sace wani.

Ba a samu jin ta bakin kakakin yan sandan jihar, DSP Sanusi Abubakar ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng