Rashin tunani ne Tinubu ya zabi Musulmi matsayin mataimakinsa: Hedkwatar Cocin Katolika

Rashin tunani ne Tinubu ya zabi Musulmi matsayin mataimakinsa: Hedkwatar Cocin Katolika

  • Darikun addinin Kirista daban-daban na cigaba da gargadin jam'iyyun APC da PDP kada su zabi Musulmi mataimaki
  • Darikar Katolika a nata jawabin ta bayyana cewa zaben Musulmi shugaba kuma Musulmi mataimaki rashin tunani ne
  • Yau ko gobe jam'iyyar APC, PDP, LP a NNP zasu sanar da wanda zai yiwa yan takararsu mataimaki

Abuja - Hedkwatar Cocin Katolika a Najeriya ta bayyana rashin amincewarta da yunkurin Musulmi da Musulmi suyi shugaban kasa da mataimaki a zaben 2023.

Cocin ta bayyana matsayarta ranar Talata ne a jawabin da Sakatare Janar dinta, Zacharia Nyantiso Samjumi, ya fitar, rahoton TheCable.

A jawabin, cocin tace wajibi ne dukkan jam'iyyun siyasa su fahimci cewa hadin kan Najeriya ya dogara ne kan daidaito tsakanin addinai.

Jawabin yace ko lokacin mulkin Soja, da tsarin Musulmi-Kirista akayi amfani.

Kara karanta wannan

Yau ko gobe Juma'a: Ganduje, Shettima, da mutum biyu da ake sa ran Tinubu zai zaba, Majiya

Catholics
Rashin tunani ne Tinubu ya zabi Musulmi matsayin mataimakinsa: Hedkwatar Cocin Katolika Hoto: Presidency

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yace:

"Misali, an yi mulkin Murtala-Obasanjo, Obasanjo-Yar'adua, Babangida-Ebitu Ukiwe, Abacha – Diya. Hakazalika shugabannin hukumomi daban-daban irinsu Kwastam, Immigration, dss."
"Lokacin mulkin Sojan Buhari kadai aka samu Musulmi da Musulmi. Hakazalika lokacin zaben Abiola-Kingibe."
Cocin tace asali bai kamata wannan ya zama matsala ba idan kan yan Najeriya a hade yake, amma kan yan Najeriya yanzu ya rabu kashi-kashi."
"Dubi ga rabuwar kai dake tsakanin yan kasar nan, Tikitin Musulmi-Musulmi ba karamin rashin tunani zai zama ba. "
"Dubi ga abinda ya faru a Kaduna, da alamun irin wahalan da Kiristocin kudancin Kaduna suka sha zai sake faruwa."

Cocin ta karkare jawabinta da kira ga jam'iyyun siyasa kada su sake su zabi abokin takara Musulmi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng

Tags: