Da Dumi-Dumi: Sojoji sun ragargaji yan ta'addan ISWAP, Sun tashi kasuwa da sansanonin su a Borno

Da Dumi-Dumi: Sojoji sun ragargaji yan ta'addan ISWAP, Sun tashi kasuwa da sansanonin su a Borno

  • Jami'an tsaro sun yi nasarar halaka yan ta'addan kungiyar ISWAP da dama a yankin Gurzum da ke jihar Borno
  • Hukumar sojojin Najeriya, ranar Laraba da safe, ta bayyana cewa dakarun sun lalata kasuwa da sansanin yan ta'addan yayin samamen
  • Hakanan Sojojin tare da haɗin guiwa dakarun CJTF sun kwato makamai da wasu kayan amfanin yan ta'adda

Borno - Hukumar sojojin Najeriya ta bayyana cewa dakarun tsaro sun samu nasarar halaka yan ta'addan kungiyar ISWAP da dama a yankin Gurzum na jihar Borno.

Hukumar ta ce rundunar Operation Desert Sanity da haɗin guiwar dakarun haɗaka na Civilian Joint Task Forces sun tashi kasuwa da wasu sansanonin yan ta'addan a yankin.

Sojoji sun halaka yan ta'adda a Borno.
Da Dumi-Dumi: Sojoji sun ragargaji yan ta'addan ISWAP, Sun tashi kasuwa da sansanonin su a Borno Hoto: @HQNigerianArmy
Source: Twitter

Wannan na ƙunshe a wani rubutu mai haɗe da hotuna da hukumar sojojin Najeriya ta saki a shafinta na tuwita ranar Laraba da safe.

Kara karanta wannan

Kano: Yadda 'Dan Ta'addan ISWAP ya Samu Gidan Zama, Ya Siya Filaye 5 da Taimakon Jami'in Hisbah

Ta ce a kokarin dawo da zaman lafiya mai ɗorewa jami'an tsaron ba tare da gajiya wa ba suna cigaba da kai wa yan ta'addan zafafan hare-hare.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bugu da ƙari, hukumar sojin ta ce jami'an tsaron sun kuma yi nasarar kwato manyan makamai, da sauran kayan aikin yan ta'addan, yayin wannan ɗauki ba daɗin.

A sanarwan Tuwita da hukumar sojin ta fitar wanda ya ƙunshi hotunan gawarwakin wasu yan ta'addan da sansanin su da aka lalalata, ta ce:

"A cigaba da hana yan ta'adda sakat da rundunar Operation Desert Sanity ke yi tare da taimakon CJTF sun samu gagarumar nasara a ranar 14 ga watan Yuni, 2022.
"Sun yi nasarar halaka yan ta'addan ƙungiyar ISWAP da dama a yankin Gurzum na jihar Borno. Kasuwar yan ta'addan da sansanonin su sun tashi aiki kuma sun kwato makamai da sauran kayan amfani."

A wani labarin na daban kuma Sojoji sun gano wata mata da Boko Haram suka sace tun 2014

Dakarun runduna ta 26 Task Force Brigade, a ranar Talata, sun gano wata wata Mary Ngoshe, wacce a cewar rundunar sojin Najeriya, tana daya daga cikin ‘yan matan da aka sace a Chibok tunshekarar 2014.

Kara karanta wannan

Sojoji da yan sanda sun yi kazamin artabu da yan bindiga a hanyar Kaduna-Abuja, rai ya salwanta

Ngoshe, wadda aka same ta da wani yaro da ake kyautata zaton nata ne, sojojin sun tare ta ne a lokacin da suke sintiri a kewayen Ngoshe a jihar Borno.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262