Shugaban majalisar dinkin Duniya ya fadawa Shugaba Buhari sirrin yakar ‘Yan ta’adda

Shugaban majalisar dinkin Duniya ya fadawa Shugaba Buhari sirrin yakar ‘Yan ta’adda

  • Shugaban majalisar dinkin Duniya ya kawo wata ziyarar gani da ido zuwa yankin Arewacin Najeriya
  • Mista Antonio Guterres ya hadu da Muhammadu Buhari a fadar Aso Villa a kan batun rashin tsaro
  • Guterres ya kawo shawarar hanyar da za a bi domin a wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali

Abuja - Shugaban majalisar dinkin Duniya, Antonio Guterres ya nuna muhimmancin komawa tushe wajen yakar ta’addancin da ke addabar Najeriya yau.

Jaridar Daily Trust ta ce Antonio Guterres ya yi wannan bayani ne da yake amsa tambaya daga wajen menama labarai a fadar Aso Villa da ke birnin Abuja.

Guterres ya yi zama da Mai girma Muhammadu Buhari, bayan nan kuma ya hadu da ‘yan jarida.

Shugaban majalisar dinkin Duniyan ya yi bayanin kokarin da su keyi wajen taimakawa gwamnatocin Afrika wajen murkushe masu tada kafar baya.

Kara karanta wannan

Rokon da Shugaba Buhari ya yi, ya fada a kan kunnen kashi, ASUU ta cigaba da yajin-aiki

Jawabin Mista Antonio Guterres

“Abu ne mai sauki, na gani a Borno. Idan ka yaki ta’addanci da karfin bindiga zalla, ‘yan ta’adda za su dawo su yake ka.”

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Shugaban majalisar dinkin Duniya
Antonio Guterres a Abuja Hoto: dailytrust.com
Asali: UGC

“Amma idan aka yaki ‘yan ta’adda da karfin bindiga da kuma bibiyar tushen ta’addancin, ba za su samu damar cigaba ba.”
“Ina tunanin Mao Tse Tung ne yake cewa tada zaune-tsaye yana yawo ne tamkar yadda kifi yake iwo a cikin ruwa.”
“Idan mutane su ka iya kare su, su ka yarda da gwamnatocinsu, kuma aka kawo tsare-tsare, za a iya magance ta’addanci.”

- Antonio Guterres

A yafewa tsofaffin 'yan ta'adda

Daga cikin tsare-tsaren da za su kawo zaman lafiya a cewar Guterres akwai karbar tsofaffin ‘yan ta’addan da suka ajiye makamai, a sama masu sabuwar rayuwa.

Guterres ya ce dole ne a tabbatarwa wadanda rikicin ta’addanci ya rutsa da su cewa su na da makoma. Vanguard ta tabbatar da haka a wani rahoto da aka fitar.

Kara karanta wannan

An yi ram da mai mulki a Kaduna yana dauke da AK-47 kusa da sansanin ‘Yan bindiga

Zuwan shugaban majalisar dinkin Duniyan Najeriya ya taimaka masa wajen sanin asalin mawuyacin halin da ‘yan gudun hijira da sauran mutane ke ciki.

Zulum zai yi takara

An ji cewa an samu wasu kungiyoyi masu zaman kansu da suka tarawa Babagana Umara Zulum kyautar N50m.

Wadannan kungiyoyi sun ba Gwamna Zulum gudumuwa ne saboda jin dadin aikin da ya ke yi a jihar Borno

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng

Online view pixel