Jerin jihohin Najeriya 24 da basu samu masu zuba hannu jari daga kasashe waje ko daya ba

Jerin jihohin Najeriya 24 da basu samu masu zuba hannu jari daga kasashe waje ko daya ba

  • Hukumar lissafin Najeriya ta saki rahoton zuba hannun jari daga kasashen waje da aka samu a shekarar 2021
  • A cewar rahoton, Najeriya bata taba samun karancin masu zuba hannun jari irin wannan ba cikin shekaru 11
  • Zuba hannun jarin attajirai daga kasashen waje ne daya daga cikin hanyoyi uku da kudi ke shigowa Najeriya

Hukumar lissafin tarayya NBS ta wallafa rahoton zuba hannun jari daga kasashen waje da jihohin Najeriya suka samu a shekarar 2021.

Legit.ng ta tattaro cewa a rahoton da aka saki, Najeriya ta samu kudi $698.7m na hannun jarin da yan kasashen waje suka zuba.

Zuba hannun jarin daga kasashen waje ne daya daga cikin hanyoyi uku da kudi ke shigowa Najeriya

A cewar rahoton da lissafi na NBS, kudin da aka samu a 2021 ne mafi karancin da Najeriya ta samu cikin shekaru 11.

Kara karanta wannan

Abubuwa 7 da ya kamata a sani a tarihin Sanata Dansadau wanda ya tsige Imam Nuru Khalid

Gwamnoni
Jerin jihohin Najeriya 24 da basu samu masu zuba hannu jari daga kasashe waje ko daya ba Hoto: Photo credit: @GovKaduna, @benuestategovt, @Hope_Uzodimma1, @Zamfara_state
Asali: Twitter

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Ga jerin jihohi 24 da basu samu masu zuba hannun jari ko guda ba a 2021:

1. Adamawa

2. Bauchi

3. Bayelsa

4. Benue

5. Borno

6. Cross River

7. Ebonyi

8. Edo

9. Enugu

10. Gombe

11. Imo

12. Jigawa

13. Kaduna

14. Katsina

15. Kebbi

16. Kogi

17. Nasarawa

18. Niger

19. Ondo

20. Plateau

21. Sokoto

22. Taraba

23. Yobe

24. Zamfara

An kashe N1.3trn amma wutar lantarki bata gyaru ba, ministar kudi

A wani labarin kuwa, ministar kasafin kudi da tsare-tsare, Zainab Ahmed, ta ce kudade Naira tiriliyan 1.3 da gwamnatin tarayya ta tanadar a bangaren samar da wutar lantarki basu haifar da da mai ido ba, inji rahoton TheCable.

A ranar 1 ga Maris, 2017, FG ta amince da kashe N701bn domin inganta wutar lantarki ga Kamfanin Dillalan Wutar Lantarki ta Najeriya (NBET) domin biyan kudin da GenCos ke samarwa ga ma’aikatar wuta ta kasa na tsawon shekaru biyu.

Kara karanta wannan

Jami'an 'yan sanda sun ki karbar cin hancin N500k bayan kama mota dankare da miyagun kwayoyi

An bayar kudaden ne domin tunkarar kalubalen kudi na wata-wata da GenCos ke fuskanta, yayin da kamfanonin rarraba wuta (DisCos) ke ci gaba da gazawa wajen biyan kudaden wutar lantarkin da ake rarrabawa duk wata.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng