Innalillahi: Yara Biyu Sun Mutu Yayin Da Banɗaki Ya Rufta a Jihar Neja

Innalillahi: Yara Biyu Sun Mutu Yayin Da Banɗaki Ya Rufta a Jihar Neja

  • Wasu kananan yara, namiji da mace sun riga mu gidan gaskiya sakamakon gini da ya rufta musu a wata makaranar frimare a Jihar Neja
  • A halin yanzu dai ba a tantance ainihin abin da ya kai kananan yaran kusa da ginin da dama aka ce ya tsufa ba har abin ya faru
  • Wasu majiyoyi sun ce yaran sun tafi wurin suna wasa ne yayin da abin ya faru wasu kuma sun ce sun je neman kayan gwangwan ne

Jihar Niger - An tsinci gawar wasu yara biyu a baraguzan wani bandaki da makarantar frimari ta tunawa da UK Bello, a Paiko, karamar hukumar Paikaro na Jihar Niger, Daily Trust ta rahoto.

A halin yanzu ba a tabbatar da abin da yaran ke yi ba a wurin yayi da ginin da aka ce ya tsufa dama ya rufta musu.

Kara karanta wannan

Kungiyar Izala ta rabawa yan gudun Hijra da matsalar tsaro ta shafa a Neja kayayayyki

Innalillahi: Yara Biyu Sun Mutu Yayin Da Banɗaki Ya Rufta a Jihar Neja
Yara Biyu Sun Mutu Yayin Da Banɗaki Ya Rufta a Jihar Neja. Hoto: Daily Trust
Asali: Twitter

Wasu majiyoyi sun ce yaran, namiji da mace, suna tallar Pure water ne tare da abokansu a kusa da makarantar a lokacin da ginin ya rufta musu, suka mutu nan take, rahoton Daily Trust.

Wasu sun ce yaran suna roron kayayyakin karafuna ne da za su sayar a kusa da ginin a lokacin da ya rufa.

Saurari karin bayani ...

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164

Tags: