Fashola: Gwamnati za ta karasa manyan ayyukan da ta tattago kafin Buhari ya sauka

Fashola: Gwamnati za ta karasa manyan ayyukan da ta tattago kafin Buhari ya sauka

  • Babatunde Raji Fashola SAN ya yi alkawarin kammala hanyar Abuja-Kaduna-Kano nan da 2023
  • Ministan ya ce kafin Muhammadu Buhari ya tafi za a gama dagar Neja da hanyar Legas-Ibadan
  • Ministar kudi ta bayyana shirin Gwamnatin tarayya na kashe har Naira tiriliyan 1.4 a kan ayyuka

FCT, Abuja - Ministan ayyuka na kasa, Babatunde Raji Fashola SAN ya ce za a gama titin Abuja-Kano, da na Legas-Ibadan da gadar Neja nan da watanni 12.

A ranar Talata, jaridar Leadership ta rahoto Ministan ayyukan yana mai wannan bayani a wajen wani taron ganawa da jama’a da aka shirya a garin Abuja.

Ma’aikatar yada labarai da raya al’adu ta hada wannan taro kamar yadda ta saba yi domin bayyana irin nasarorin da gwamnatin nan mai-ci ta samu.

Kara karanta wannan

Alkali ya bada umarni hukumar EFCC ta karbe gidan tsohon Gwamnan APC a Abuja

Ministan ya ce ma’aikatarsa ta bada kwangilolin tituna 1, 018 na ayyuka 859 a jihohi 36 da garin Abuja. Jaridar nan ta Vanguard ta fitar da irin wannan rahoton.

Muhimman ayyuka 3

A cewar Ministan, gwamnatin tarayya za tayi kokari wajen ganin ta kammala duka wadannan manyan ayyuka kafin wa’adin Muhammadu Buhari ya cika.

Ana kokarin fadada titin Abuja-Kaduna-Kano wanda zai hada jihohin Arewacin Najeriya da birnin tarayya Abuja. A halin yanzu wannan aiki yana ta tafiya.

Aikin titi
Hanyar Legas zuwa Ibadan Hoto: www.julius-berger.com
Source: UGC

Baya ga haka akwai babban titin Legas zuwa Ibadan wanda an dade da fara aikin. Sai kuma gadar nan ta 2nd Niger wanda ta hada 'Yan Neja-Delta da kasar Ibo.

Shirin da muke yi a 2022 - Zainab Ahmed

A wajen wannan taro, Ministar kudi, kasafi da tsare-tsaren tattalin arziki, Zainab Ahmed ta samu damar yin jawabi, ta bayyana irin nasarorin da suka samu.

Zainab Ahmed ta ce gwamnatin tarayya ta fi maida hankali wajen kashe kudi a kan samar da abubuwan more rayuwa domin inganta tattalin arzikin kasa.

Kara karanta wannan

Abubuwa 10 da Kwankwaso ya fada wajen kaddamar da sabuwar tafiyar siyasarsu

A wajen wannan taro, an ji cewa Najeriya za ta kashe kimanin Naira tiriliyan 1.42 a bana. Sannan gwamnati za a kashe Naira tiriliyan 2.11 wajen raya mutane.

EFCC v Okorocha

Dazu nan ku ka ji cewa hukumar EFCC ta fara samun nasara a kan Rochas Anayo Okorocha, Alkali ya bukaci a karbe wani gidan da ya mallaka a Abuja.

Hukumar EFCC ta na zargin cewa da kudin gwamnatin Imo aka saye gidan, don haka kotu ta ce a karbe gidan sai sun karkare shari’a a babban kotun tarayyar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng