Jerin sunaye da ma'aikatu: Matawalle ya ƙirƙiri sabbin ma'aikatu 4, ya sauya wa kwamishinoni wurin aiki

Jerin sunaye da ma'aikatu: Matawalle ya ƙirƙiri sabbin ma'aikatu 4, ya sauya wa kwamishinoni wurin aiki

  • Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle ya amince da kafa wasu ma’aikatu 4 na daban a jihar
  • Bayan kafa ma’aikatun ya kuma zabo sabon kwamishina ga ko wacce sabuwar ma’aikata
  • Ya kafa ma’aikatar kula da dajika da dabbobin kiwo, da ta samar da dukiya da ayyukan yi da sauran biyu

Jihar Zamfara - Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle ya tabbatar da samar da ma’aikatu 4 sannan ya zabo sababbin kwamishinoni na ma’aikatun.

Ya bayyana hakan ne ta wata takarda wacce sakataren gwamnatin jihar, Kabiru Balarabe ya bayyana a Gusau ranar Litinin bisa ruwayar The Punch.

Jerin sunaye da ma'aikatu: Matawalle ya ƙirƙiri sabbin ma'aikatu 4, ya sauya wa kwamishinoni wurin aiki
Gwamna Bello Matawalle na jihar Zamfara. Hoto: The Punch
Asali: Facebook

A cewar Balarabe, ma’aikatun da ya kafa guda 4 su ne:

Kara karanta wannan

Shekara daya da rabi da Shugaba Buhari ya yi magana, har yau umarninsa bai fara aiki ba

  • Ma’aikatar kula da dazuka da bunkasa kiwon dabobbi
  • Ma’aikatar samar da dukiya da kuma samar da ayyuka.
  • Ma’aikatar yawon bude ido da kula da otal da kuma
  • Ma’aikatar gina gidaje da bunkasa birane

Balarabe ya bayyana yadda gwamnatin ta nada sababbin kwamishinoni wadanda za su fara aiki daga nadin.

Ya lissafo ma’aikatun da kwamishinonin kamar haka;

  1. Ahmed Anka - Ma’aikatar ilimin kimiyya da fasaha
  2. Abubakar Dambo - Ma’aikatar harkokin kananun hukumomi
  3. Muh’d Magaji - Ma’aikatar al’adu
  4. Nasiru Masama - Ma’aikatar matasa da bunkasa wasanni
  5. Abdulaziz Nahuce - Ma’aikatar ayyuka na musamman
  6. Zainab Gummi - Ma’aikatar ilimi.
  7. Sufyan Yuguda - Ma’aikatar kudi
  8. Fa’eka Marshal - Ma’aikatar harkokin jin kai da annoba
  9. Rabiu Gusau - Ma’aikatar ayyuka da tafiye-tafiye
  10. Yazeed Fulani - Ma’aikatar sana’o’i da ma’aikatu
  11. Ibrahim Gusau - Ma’aikatar dazuka da bunkasa kiwon dabbobi
  12. Nuradden Gusau - Ma’aikatar ma’adanai
  13. Junaidu Kaira - Ma’aikatar shari’a
  14. Akwai Ibrahim Magayaki - Ma’aikatar noma
  15. Ibrahim Dosara - Ma’aikatar labarai
  16. Yahaya Gora - Ma’aikatar ilimin gaba da sakandare
  17. Yahaya Kanoma - Ma’aikatar samar da ayyuka da bunkasa arziki
  18. Lawal Badarawa - Ma’aikatar bunkasa al’umma
  19. Sheikh Jangebe - Ma’aikatar harkokin addini
  20. Aliyu Tukur - Ma’aikatar kasafi da tsari,
  21. Aliyu Tsafe - Ma’aikatar lafiya,
  22. Mamman Tsafe - Ma’aikatar tsaro da harkokin cikin gida,
  23. Abubakar Tsafe - Ma’aikatar yawon bude ido da kula da otal
  24. Ibrahim Mayana - Ma’aikatar ruwa
  25. Abubakar Bore - Ma’aikatar bunkasa kauyaku.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164