Jami’an tsaro sun kama matar da ta rufe ‘yar shekara 6 a daki na wata da watanni

Jami’an tsaro sun kama matar da ta rufe ‘yar shekara 6 a daki na wata da watanni

  • ‘Yan sandan jihar Osun sun kama wata mata da ta rufe karamar yarinya na tsawon watanni a gida
  • Rahotanni sun ce Olanrewaju Adenike ta garkame wata ‘yar shekara shida ne a wani kazamin daki
  • Makwabtanta a Isale-Osun sun samu labarin abin da yake faruwa, sai su ka sanar da jami’an tsaro

Osun - Rundunar ‘yan sandan Najeriya na reshen jihar Osun, sun ceto wata karamar yarinya mai suna Aishat Taiwo daga hannun mai kula da ita.

Daily Trust ta kawo rahoto a ranar Laraba, 1 ga watan Disamba, 2021 cewa wannan mata mai suna Olanrewaju Adenike ta tsare Aishat Taiwo a daki.

Adenike ta rufe wannan yarinya mai shekara shida a cikin wani kazamin daki na tsawon watanni, an ce dakin ya na kusa da wani kewaye.

Jaridar ta rahoto Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Osun, Wale Olokode, yana cewa Olanrewaju Adenike ta gallazawa Taiwo azaba kafin ta kubuta.

Kara karanta wannan

'Yan banga sun jawo 'yan bindiga sun hallaka mazauna a Sokoto, gwamnati ta fusata

Olokode ta bakin mai magana da yawun bakin rundunar ‘yan sanda na Osun, Yemisi Opalola ya bayyana yadda asirin wannan Baiwar Allah ya tonu.

Jami’an tsaro
Dakarun 'Yan sanda Hoto: www.bbc.com
Asali: UGC

Ceto ya zo wa Aisha Taiwo

Wasu mutane ne suka sanar da jami’an ‘yan sanda game da irin azabar da Olanrewaju Adenike ta ke yi wa wannan yarinya da ta rufe a cikin gidanta.

Makwabtan wannan mata da yanzu ta ke hannu a unguwar Isale-Osun, a yankin Osogbo a jihar Osun ne suka sanar da ‘yan sanda halin da ake ciki.

Halin da yarinyar ta ke ciki

Mai girma kwamishinan ‘yan sanda, Olokode ya shaidawa manema labarai cewa yarinyar ta na hannunsu a halin yanzu, kuma ta na samun kulawa.

Baya ga haka, CP Olokode ya tabbatar da cewa rundunar ‘yan sanda na jihar Osun, su na kokarin gano iyayen ta domin a maida ta karkashin kulawarsu.

Kara karanta wannan

Rikicin Goje da Inuwa: Kotu ta tasa keyar hadimin Goje zuwa kotu saboda yin rubutu a Facebook

Ba a ji ta bakin wannan mata domin sanin abin da ya sa ta yi wannan aiki ba, kuma ‘yan sanda ba su yi bayanin irin matakin da za su dauka a kanta ba.

Masu garkuwa da mutane

A garin Zaria, jihar Kaduna, an ji 'yan bindigan da suka yi garkuwa da wasu ma'aikata sun fito da mutum 10, an tsare 3 saboda ba su cika sharuda ba.

Miyagun ‘Yan bindigan sun ce ba za su saki mutanen da suka sace a garin Giwa ba sai an ba su kudi Naira miliyan 40 da kuma sababbin babura uku.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng