Jerin jami'o'i 10 da dalibai suka fi nema a Najeriya, Hukumar JAMB, Ta farko na Arewa

Jerin jami'o'i 10 da dalibai suka fi nema a Najeriya, Hukumar JAMB, Ta farko na Arewa

  • Hukumar JAMB ta saki lambar adadin daliban da suka nemi shiga jami'a bana
  • Manyan jami'o'in Arewa daga Arewa na cikin jami'o'i goma da aka fi nema
  • Jami'ar Ilori dake jihar Kwara, Arewa maso tsakiyar Najeriya ce ta farko

Abuja - Hukumar shirya jarabawar shiga jami'a, JAMB, ta bayyana cewa jami'ar Ilori da jami'ar Legas, Akoka ne jami'o'i biyu da dalibai sukafi neman shiga a Najeriya.

Wannan na kunshe cikin takardar rahoton hukumar da shugaban hukumar, Farfesa Ishaq Oloyede, ya rattafa hannu, Punch ta samu.

Rahoton ya yi bayanin adadin daliban da suka nemi gurbin shiga kowace jami'a da kuma adadin makin da suka samu.

Rahoton yace a jarabawar 2021 da aka zana, mutum 1,312,992 ne suka zauna jarabawar UTME. Yayinda mutum 168,613 suka samu maki 200 da abinda yayi sama; mutum 236,936 kuma ci 190-200.

Kara karanta wannan

Jerin kamfanoni 14 mallakin gwamnati da shugaba Buhari zai sayar saboda dalilai

Hakazalika mutum 327,624 sun samu 180 zuwa 190, kuma mutum 445,597 sun ci 170 - 179.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Jerin jami'o'i 10 da dalibai suka fi nema a Najeriya, Hukumar JAMB
Jerin jami'o'i 10 da dalibai suka fi nema a Najeriya, Hukumar JAMB Hoto: BUK
Asali: Twitter

Ga jerin jami'o'in 10 da dalibai suka fi nema da adadin mutanen da suka nema:

1. Jami'ar Ilori (UNILORIN) - 78,466

2. Jami'ar Legas (UNILAG) - 59,190,

3. Jami'ar Benin, (UNIBEN) - 49,763;

4. Jami'ar Najeriya (UNN) - 47,239;

5. Federal University, Oye-Ekiti, 45,920;

6. Jami'ar Ahmadu Bello Zaria (ABU) - 44,509;

7. Jami'ar Bayeri Kano (BUK) 44,352;

8. Jami'ar Nnamdi Azikiwe - 43542;

9 Jami'ar Obafemi Awolowo - 42, 614

10. Jami'ar Jos (UNIJOS) - 38,309.

Yajin-aiki: A zargi Gwamnatin Najeriya idan muka dauki mataki na gaba inji Kungiyar ASUU

Kungiyar malaman jami’a na kasa, ASUU, ta fara maganar kiran taron gaggawa na majalisar koli ta NEC a makon nan, domin tayi zama.

Kara karanta wannan

Isa Pantami ya zama Farfesan Jami'a yana rike da kujerar Ministan Gwamnati a Najeriya

Jaridar The Nation ta ce hakan ya zama dole ne bayan wa’adin da kungiyar ta ASUU ta ba gwamnatin tarayya ya cika a karshen watan Agusta.

Bayan wannan zama, ASUU tace za ta tattauna da duk masu fada-a-ji a duka rassan kungiyar, idan dai gwamnati ta gaza cika alkawuran da ta dauka.

Asali: Legit.ng

Online view pixel