Abubuwa 6 da ya dace a sani a game da sabon Hukumar NCDC da Shugaban kasa ya nada

Abubuwa 6 da ya dace a sani a game da sabon Hukumar NCDC da Shugaban kasa ya nada

  • Dr. Ifedayo Morayo Adetifa zai dare kujerar Darekta-Janar a hukumar NCDC
  • Rahotanni sun bayyana cewa Dr. Adetifa ya yi karatu a Najeriya da Amsterdam
  • Sabon Darektan ya kusa zama Farfesa a wata makarantar tsabta da ke Landan

Abuja - Shugaba Muhammadu Buhari ya nada Dr. Ifedayo Morayo Adetifa a matsayin Darekta-Janar na hukumar NCDC mai yaki da cututtuka a Najeriya.

Daily Trust ta tsakuro wasu abubuwa daga cikin tarihin sabon shugaban hukumar ta NCDC.

Ga wasu kadan daga cikin tarihin wannan kwararren likita wanda zai dare kujerar hukumar NCDC.

1. A ina yayi karatun digirin farko?

Ifedayo Morayo Adetifa ya samu digirin likitanci a jami’ar Ilorin da ke Kwara. Sannan ya samu hora a fannin duba kananan yara a asibitin koyon aiki na LUTH. A 2005 ne kungiyar likitoci ta Afrika ta yamma ta tabbatar da shi a matsayin kwararren likitan yara.

Kara karanta wannan

Shugaban kasa ya yi sabon nadi, ya ba Osinbajo sabon aiki, ya nada shugaba a hukumar NCDC

2. Ya yi digirgir da digir-digir a Amsterdam

Rahoton yace sabon shugaban na NCDC ya karanci ilmin karantar yadda cututtuka suke yadu wa al’umma a jami’ar Amsterdam, kasar Netherlands. A nan ya samu digirinsa na biyu da na uku.

3. Farfesa a makarantar Landan

Kafin ya samu wannan mukami a Najeriya, likitan ya kai matakin mataimakin Farfesa a cibiyar kula da cututtuka a makarantar tsabta da manyan cututtuka da ke Landan a kasar Ingila.

NCDC DG
Ifedayo Morayo Adetifa Hoto: dailytrust.com
Asali: UGC

4. A wani bangare ya yi bincike da nazari?

A tsawon shekarun da ya yi yana karatu, Dr. Ifedayo Morayo Adetifa ya fi bada karfi wajen bincike a kan karfin magungunan cututtuka, dabarun rigakafi, da yadda cutar tarrin tibi ta ke yadu wa

5. Kungiyar MRC/DFID

A 2018 aka shigar da Morayo Adetifa cikin kungiyar MRC/DFID ta kwarrarun masu bincike a nahiyar Afrika. Sannan likitan ya na cikin kwamitin rigakafi da WHO ta kafa a kasar Kenya.

Kara karanta wannan

Isa Pantami ya zama Farfesan Jami'a yana rike da kujerar Ministan Gwamnati a Najeriya

6. Aikin rigakafin cututtuka

Bayan haka, Dr Ifedayo Morayo Adetifa ya taka rawar gani a kwamitin kula da rigakafi a Kenya, da majalisar RITAG ta kungiyar WHO da kwamitin da aka ba nauyin rigakafin masassara a Afrika.

Kamar yadda kuka ji labari, Ifedayo Morayo Adetifa zai maye gurbin Dr. Chikwe Ihekweazu, wanda ya samu kujera a mai tsoka a kungiyar lafiya ta Duniya.

Shugaban WHO, Tedros Ghebreyesus ya aiko wa Chikwe Ihekweazu takarda yana sanar da shi zai rike kujerar shugaban sashen bada agajin gaggawa a kungiyar.

Asali: Legit.ng

Online view pixel