Da duminsa: 'Yan majalisa sun tsige kakakin majalisar jihar Kebbi

Da duminsa: 'Yan majalisa sun tsige kakakin majalisar jihar Kebbi

  • An tsige Honarabul Ismaila Abdulmummuni Kamba, kakakin majalisar jihar Kebbi da mataimakinsa, Muhammadu Buhari Aliyu daga kujerunsu
  • An nada Muhammad Abubakar Lolo mai wakiltar yammacin Bagudo a matsayin sabon kakakin da kuma Mohammed Usman Zuru a matsayin mataimakinsa
  • Sai da 'yan majalisar guda 20 cikin 24 suka amince da tsige su daga kujerun nasu kafin hakan ya tabbata

Birnin Kebbi, Kebbi - An tumbuke Honarabul Abdulmummuni Kamba, kakakin majalisar jihar Kebbi da mataimakinsa, Muhammadu Buhari Aliyu daga kujerunsu.

Daily Trust ta ruwaito cewa, sai da 'yan majalisar 20 cikin 24 suka amince kafin a tsigesu daga madafun ikon nasu.

Yanzu haka an daura Muhammad Abubakar Lolo, dan majalisa mai wakiltar Bagudo ta yamma a matsayin kakakin majalisar, sannan Muhammad Usman Zuru mai wakiltar mazabar Zuru ya zama mataimakinsa.

Kara karanta wannan

Lady Adanma, matar Michael Okpara, tsohon firemiyan yankin gabas ta rasu

Da duminsa: 'Yan majalisa sun tsige kakakin majalisar jihar Kebbi
Da duminsa: 'Yan majalisa sun tsige kakakin majalisar jihar Kebbi
Asali: Original

Karin bayani na nan tafe...

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164