Da duminsa: 'Yan majalisa sun tsige kakakin majalisar jihar Kebbi

Da duminsa: 'Yan majalisa sun tsige kakakin majalisar jihar Kebbi

  • An tsige Honarabul Ismaila Abdulmummuni Kamba, kakakin majalisar jihar Kebbi da mataimakinsa, Muhammadu Buhari Aliyu daga kujerunsu
  • An nada Muhammad Abubakar Lolo mai wakiltar yammacin Bagudo a matsayin sabon kakakin da kuma Mohammed Usman Zuru a matsayin mataimakinsa
  • Sai da 'yan majalisar guda 20 cikin 24 suka amince da tsige su daga kujerun nasu kafin hakan ya tabbata

Birnin Kebbi, Kebbi - An tumbuke Honarabul Abdulmummuni Kamba, kakakin majalisar jihar Kebbi da mataimakinsa, Muhammadu Buhari Aliyu daga kujerunsu.

Daily Trust ta ruwaito cewa, sai da 'yan majalisar 20 cikin 24 suka amince kafin a tsigesu daga madafun ikon nasu.

Yanzu haka an daura Muhammad Abubakar Lolo, dan majalisa mai wakiltar Bagudo ta yamma a matsayin kakakin majalisar, sannan Muhammad Usman Zuru mai wakiltar mazabar Zuru ya zama mataimakinsa.

Kara karanta wannan

Lady Adanma, matar Michael Okpara, tsohon firemiyan yankin gabas ta rasu

Da duminsa: 'Yan majalisa sun tsige kakakin majalisar jihar Kebbi
Da duminsa: 'Yan majalisa sun tsige kakakin majalisar jihar Kebbi
Asali: Original

Karin bayani na nan tafe...

Asali: Legit.ng

Online view pixel