Magoya-baya suna zugo Ministan Buhari ya fito takarar Shugaban kasa a APC a 2023
- Kungiyar 'Senator Akpabio for Common Good' ta wanke Ministan Neja-Delta
- Ana zargin cewa tsoron hukumar EFCC ya sa Godswill Akpabio ya koma APC
- Wannan kungiya ta kare Ministan, tana nema masa goyon baya a zaben 2023
Abuja - Wata kungiyar siyasa mai suna Senator Akpabio for Common Good, ta na jan-kunnen ‘yan adawan tsohon gwamnan Akwa-Ibom, Godswill Akpabio.
Jaridar Leadership ta kawo rahoto cewa kungiyar Senator Akpabio for Common Good ta yi kira ga mau kokarin bata sunan Godswill Akpabio, su yi hattara.
A wani jawabi da shugaban kungiyar na kasa, Malam Jibril Tafida, ya fitar, ya yi kira ga Ministan harkar Neja-Deltan ya yi takarar shugaban kasa a zaben 2023.
Da yake jawabi a ranar Litinin, 23 ga watan Agusta, 2021, Malam Jibril Tafida yace ba a taba samun gwaninsu, Ministan da wani laifin rashin gaskiya ba.

Kara karanta wannan
Kungiyar kare hakkin jama'a ta kai karar Buhari a kotu kan ‘bacewar’ Naira Biliyan 106 a 2018
Saboda EFCC Akpabio ya tsere daga PDP?
Rahoton yace kungiyar ta fitar da wannan jawabi a lokacin da ake rade-radin Ministan ya koma jam’iyyar APC ne domin gudun hukumar EFCC ta bincike shi.
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Tafida ya wanke Godswill Akpabio daga zargin da ake yi masa, yake cewa Ministan na Neja-Delta ya sauya-sheka daga jam’iyyar PDP ne domin ganin damansa.

Asali: UGC
Vanguard ta rahoto shugaban kungiyar magoya bayan yana cewa babu wanda ya tursasa wa Akpabio.
Kungiyar Senator Akpabio for Common Good ta kuma yi gargadi a kan jifan tsohon gwamnan da zargi da nufin a bata masa suna, duk da bautar da yake yi wa kasa.
A jawabin, Tafida yace bai kamata kuma a zargi Sanata Akpabio da hannu a binciken da EFCC ke kokarin yi kan tsohon gwamnan Bayelsa, Seriake Dickson ba.
A cewar kungiyar, Ministan ya bar tarihi a lokacin da yake gwamna a Akwa Ibom, ganin yadda ya kawo gyara, ya inganta sha’anin ilmi, kiwon lafiya da wasanni.
A karshe ta yi kira ga mutane da kungiyoyi su mara wa Akpabio bayan zama shugaban kasa a 2023.
EFCC ta kyale gidan Kwankwaso
Rahotanni sun zo mana cewa jami’an EFCC sun yi maza, sun cire shingen da suka sa a daya daga cikin gidajen tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso.
Wani hadimin tsohon Ministan tsaro na kasar, ya shaida mana cewa EFCC ta goge tambarin da tayi a Amana House. A lokacin Sanata Kwankwaso ya na Abuja.
Asali: Legit.ng