Da duminsa: Shugaba Buhari ya dira birnin Yola don gaisuwar ta'aziyyar Ahmad Joda

Da duminsa: Shugaba Buhari ya dira birnin Yola don gaisuwar ta'aziyyar Ahmad Joda

  • Shugaba kasa ya tafi jihar Adamawa yau Juma'a
  • Jihar Adamawa ta yi rashin manyan 'yayanta uku a kwanakin nan

Yola - Shugaba Muhammadu Buhari ya dira birnin Yola, jihar Adamawa a ranar Juma'a, 20 ga Agusta, domin gaisuwar ta'aziyya ga iyalan marigayi Alhaji Ahmed Joda.

Buhari ya dira ne misalin karfe 10 na safe tare da tawagarsa.

Hadimin Buhari na gidajen rediyo da talabijin, Buhari Sallau, ya bayyana haka.

Dirarsa ke da wuya, Buhari ya garzaya fadar Lamidon Adamawa.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Da duminsa: Shugaba Buhari ya dira birnin Yola don gaisuwar ta'aziyyar Ahmad Joda
Da duminsa: Shugaba Buhari ya dira birnin Yola don gaisuwar ta'aziyyar Ahmad Joda
Asali: Original

Rasuwar Alhaji Ahmad Joda

Tsohon Babban Sakataren Gwamnatin Najeriya lokacin mulkin Soja kuma mutum na farko da Buhari ya ba mukami bayan nasara a 2015 , Alhaji Ahmed Joda, ya mutu.

Kara karanta wannan

Ahmad Joda bai taba neman alfarma waje na ba, Shugaba Buhari

Ya rasu ne ranar Juma'a, 13 ga Agusta a Yola, babbar birnin jihar Adamawa.

Ya rasu yana da shekara 91 a duniya.

Alhaji Ahmed Joda ya cika ne yana mai shekaru 91 a duniya.

Joda ya yi karatunsa a Najeriya da kuma Birtaniya inda ya halarci Kwalejin Pitmans da ke birnin London daga 1954 zuwa 1956.

Ya rike kujeran sakataren din-din-din lokacin gwamnatin mulkin soja ta Janar Yakubu Gowon (Mai murabus).

Asali: Legit.ng

Online view pixel