Yanzu-yanzu: Tsohon sakataren gwamnati, Alhaji Ahmad Joda, ya rasu

Yanzu-yanzu: Tsohon sakataren gwamnati, Alhaji Ahmad Joda, ya rasu

  • Allah ya yiwa tsohon sakataren din-din-din rasuwa
  • Alhaji Ahmad Joda ya yi dogon jinya a asibiti
  • Yan Najeriya da dama sun aika sakon ta'aziyya ga iyalansa

Yola - Tsohon Babban Sakataren Gwamnatin Najeriya lokacin mulkin Soja kuma mutum na farko da Buhari ya ba mukami bayan nasara a 2015 , Alhaji Ahmed Joda, ya mutu.

BBC ta ruwaito daya daga cikin 'yayan marigayin, Asma'u Joda, ta bayyana cewa mahaifinta ya rsu ne yau Juma'a a Yola, babbar birnin jihar Adamawa.

Ya rasu yana da shekara 91 a duniya.

Alhaji Ahmed Joda ya cika ne yana mai shekaru 91 a duniya.

A cewar DT, Ahmad Joda ya rasu ne bayan jinya a asibitin FMC Yola.

Joda ya yi karatunsa a Najeriya da kuma Birtaniya inda ya halarci Kwalejin Pitmans da ke birnin London daga 1954 zuwa 1956.

Kara karanta wannan

Da duminsa: Shugaba Buhari ya dawo gida bayan kimanin makonni biyu a Landan

Ya rike kujeran sakataren din-din-din lokacin gwamnatin mulkin soja ta Janar Yakubu Gowon (Mai murabus).

Yanzu-yanzu: Tsohon sakataren gwamnati, Alhaji Ahmad Joda, ya rasu
Yanzu-yanzu: Tsohon sakataren gwamnati, Alhaji Ahmad Joda, ya rasu

Shugaba Buhari ya dawo gida bayan kimanin makonni biyu a Landan

Shugaba Muhammadu Buhari ya dawo gidan Najeriya bayan zaman ganin Likita na kimanin makonni biyu da yayi a birnin Landan, kasar Birtaniya.

Buhari ya dira a Abuja ne da yammacin Juma'a, 13 ga watan Agusta, 2021.

Mai magana da yawun shugaban kasan, Femi Adesina, ya bayyana hakan da yammacin nan a shafinsa na Facebook.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng