Sarkin Musulmi ya koka kan halin yunwar da al’umma ke ciki, ya ce abubuwa na kara birkicewa

Sarkin Musulmi ya koka kan halin yunwar da al’umma ke ciki, ya ce abubuwa na kara birkicewa

  • Sultan Sa’ad Abubakar III ya yi jawabi a taron zaman lafiya da aka shirya a Gombe
  • Mai alfarma Sarkin Musulmin ya ce farashin kayan abinci suna ta tashi a Najeriya
  • Sultan yace idan jama’a suna zama da yunwa, ba za a taba samun zaman lafiya ba

Gombe - Mai alfarma Sarkin Musulmi, Mohammed Sa'ad Abubakar III, ya ce abubuwa suna kara tabarbare wa a Najeriya, ana fama da karancin abinci.

Yunwa ba ta da hankali

Sultan Mohammed Saad Abubakar III ya bayyana cewa rashin isasshen abinci ya na jawo rashin tsaro.

Punch ta rahoto Sarkin Musulmi ya na cewa yunwa ba ta da hankali yayin da yake gabatar da jawabi a ranar Alhamis, 5 ga watan Agusta, 2021 a Gombe.

Mai alfarma Sarkin Musulmi ya yi magana ne a kan hadin-kai a Najeriya a wajen wani taro da majalisar Da’wah Coordination Council of Nigeria ta shirya.

Sultan yake cewa matsalolin ‘yan Najeriya kullum dada karu wa yake yi a halin da ake ciki, Mohammed Saad Abubakar yace abubuwa ba kyau suke yi ba.

Kara karanta wannan

Da aka je aka dawo, BOT ta ceci Shugaban PDP daga yunkurin tsige shi, a nada rikon kwarya

Babu addinin da ya ce a kashe rai - Sultan

“Abin da mu ka rasa a kasar nan shi ne gaskiya da fada wa kanmu gaskiya wajen yin abin da zai fishe mu, domin babu addinin da ya ce a kashe mutum.”

Sultan of Sokoto
Sarkin Musulmi, Sultan na kasar Sokoto Hoto: Facebook
Asali: Facebook

“Ta’addanci, tada zaune-tsaye da garkuwa da mutane su na ci, kuma masu wannan aiki suna yawo abinsu.”
“Mutane da yawa suna cikin yunwa, domin ba za su iya sayen abinci ba; farashi ya na kara tashi sama kullum. A tabbatar akwai abinci saboda talaka ya samu.”
“Idan babu abinci, babu zaman lafiya, idan babu zaman lafiya, babu tsaro, idan babu tsaro, babu cigaba, idan babu cigaba, za mu rika rayuwa ne haka kurum.”

Jaridar ta ce limamin kiristan nan, John Onaiyekan ya yi jawabi a taron ta bakin Rabaren Father Joseph Shinga, inda ya yi kira ga al’umma su zauna lafiya da junansu.

Kara karanta wannan

Bakare: Abokin tafiyar Buhari ya ba shi shawarar abin yi, ya daina sukar shugabannin baya

Sauran wadanda suka tofa albarkacin bakinsu, sun hada da Sarkin Gombe, Mai martaba, Abubakar Shehu Abubakar III da gwamna, Muhammad Inuwa Yahaya.

Babu zaman lafiya a jihar Shugaban kasa

Gwamna Aminu Bello Masari ya fadi halin rashin tsaro da suke ciki, ya ce kullum sai ‘Yan bindiga sun yi wa mata fyade a kananan hukumomi 10 a jihar Katsina

Rt. Hon. Aminu Bello Masari ya ce duk ranar Allah, miyagun ‘yaan bindiga su kan yi ta’adi a jiharsa

Asali: Legit.ng

Online view pixel