Yan Najeriya su shiryawa mumunan ambaliyar ruwan sama tsakanin Agusta da Oktoba, Gwamnatin Tarayya

Yan Najeriya su shiryawa mumunan ambaliyar ruwan sama tsakanin Agusta da Oktoba, Gwamnatin Tarayya

  • Gwamnatin tarayya ta yi kira ga yan Najeriya su shiryawa mumunan ambaliya
  • An ambaci jerin jihohin da ka iya fuskantar wannan ambaliya
  • Ministan ruwa da shugaban hukumar NIHSA sunce gwamnatocin jiha su gyara magudanun ruwa

Yan Najeriya su shiryawa mumunan ambaliyar ruwan sama

Hukumar ayyukan ruwan Najeriya (NIHSA) ta yi hasashen cewa tsakanin watan Agusta da farkon Oktoba, za'ayi mumunan ambaliyan ruwan sama a Najeriya.

NIHSA tace ambaliyar zata munana a wasu jihohi da birnin tarayya Abuja, rahoton DT.

Dirakta Janar na hukumar, Injiniya Nze Clement Onyeaso, a hirar da yayi da manema labarai a Abuja, ya ce dukkan jihohin da aka ambata a farkon shekara zasu fuskanci ambaliya su shirya.

Ya yi kira ga yan Najeriya su shiryawa wannan ambaliya ta hanyar gyara magudanun ruwa tare da cire bola, ciyayi, gansakuka dss.

Yan Najeriya su shiryawa mumunan ambaliyar ruwan sama tsakanin Agusta da Oktoba
Yan Najeriya su shiryawa mumunan ambaliyar ruwan sama tsakanin Agusta da Oktoba, Gwamnatin Tarayya Hoto: Hoto: @RepKahele
Asali: Twitter

Muna hasashen za'ayi ambaliya a jihohi 28 bana, Gwamnatin tarayya ta lissafo su

Kara karanta wannan

Miyagu sun sheke dan takarar shugaban karamar hukuma na APC a Kaduna

A watan Mayu, anyi hasashen mumunan ambaliyar ruwan sama a jihohin Najeriya akalla 28 a bana, sabon rahoton hasashen ambaliya AFO ya nuna.

Ana fitar da wannan rahoto ne a kowani shekara.

Jihohin da aka lissafo sune,Abia, Akwa Ibom, Anambra, Bauchi, Bayelsa, Benue, Cross River, Delta, Ebonyi, Edo, FCT, Gombe, Imo, Jigawa, Kaduna, Kano and Kebbi, Kwara, Lagos, Nasarawa, Niger, Ogun, Oyo, Rivers, Sokoto, Taraba da Zamfara.

Ministan arzikin ruwa, Suleiman Adamu, ya lissafa wadannan jihohi ne ranar Alhamis a taron gabatar da rahoton hasashen ambaliya na shekara-shekara na hukumar ayyukan ruwa a Najeriya (NIHSA).

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng