Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby

Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby

- Bayan kisan mahaifinsa, Mahamat Debu ya dane kujerar mulkin kasar Chadi

- Hawarsa mulki ke da wuya, ya fara kai ziyara wajen shugabannin kasashen da ke mawabtaka da Chadi

- Wannan karon ya kawo ziyararsa ta farko Najeriya a ranar Juma'a

Shugaba Muhammadu Buhari a ranar Juma'a, ya karbi bakuncin dan marigayi Idris Deby, Mahamat Kaka Deby, wanda shine mukaddashin shugaban kasar Tchad.

Janar Mahamat ya dira fadar Aso Villa ne misalin karfe 11:11 na safe, rahoton TheNation.

Duk da cewa ba'a san abinda suke tattaunawa ba a yanzu, ana kyautata zaton yana da alaka da matsalar tsaro na yan ta'addan Boko Haram a yankin Sahel.

Mahamat Deby ya gaji mahaifinsa ne wanda yan tawaye kasar Chadi suka hallaka a filin daga.

Kalli hotunan:

Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby
Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby Hoto: Aso Rock
Asali: Twitter

KU KARANTA: Muna namijin kokarin wajen magance matsalar tsaro, ina fatan yan Najeriya zasu gane, Buhari

Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby
Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby Hoto: Aso ROck
Asali: Facebook

Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby
Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby Hoto: Aso ROck
Asali: Facebook

KU DUBA: Wajibi ne Buhari ya saurari abinda muke fada masa, Gwamnonin Kudu 17

Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby
Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby Hoto: Aso ROck
Asali: Facebook

A bangare guda, Shugaba Muhammadu Buhari a ranar Alhamis ya bayyana cewa gwamnatinsa na namijin kokarin wajen magance matsalar tsaron da ta addabi Najeriya.

A bayaninsa, Buhari yace yana fatan yan Najeriya zasu gane irin kokarin da sukeyi.

Buhari ya bayyana hakan ne a hira da manema labarai bayan halartan Sallar Idi a fadar shugaban kasa, Aso Villa, Abuja.

Asali: Legit.ng

Online view pixel