Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby

Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby

- Bayan kisan mahaifinsa, Mahamat Debu ya dane kujerar mulkin kasar Chadi

- Hawarsa mulki ke da wuya, ya fara kai ziyara wajen shugabannin kasashen da ke mawabtaka da Chadi

- Wannan karon ya kawo ziyararsa ta farko Najeriya a ranar Juma'a

Shugaba Muhammadu Buhari a ranar Juma'a, ya karbi bakuncin dan marigayi Idris Deby, Mahamat Kaka Deby, wanda shine mukaddashin shugaban kasar Tchad.

Janar Mahamat ya dira fadar Aso Villa ne misalin karfe 11:11 na safe, rahoton TheNation.

Duk da cewa ba'a san abinda suke tattaunawa ba a yanzu, ana kyautata zaton yana da alaka da matsalar tsaro na yan ta'addan Boko Haram a yankin Sahel.

Mahamat Deby ya gaji mahaifinsa ne wanda yan tawaye kasar Chadi suka hallaka a filin daga.

Kalli hotunan:

Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby
Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby Hoto: Aso Rock
Asali: Twitter

KU KARANTA: Muna namijin kokarin wajen magance matsalar tsaro, ina fatan yan Najeriya zasu gane, Buhari

Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby
Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby Hoto: Aso ROck
Asali: Facebook

Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby
Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby Hoto: Aso ROck
Asali: Facebook

KU DUBA: Wajibi ne Buhari ya saurari abinda muke fada masa, Gwamnonin Kudu 17

Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby
Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya karbi bakuncin sabon shugaban Chadi, Mahamat Deby Hoto: Aso ROck
Asali: Facebook

A bangare guda, Shugaba Muhammadu Buhari a ranar Alhamis ya bayyana cewa gwamnatinsa na namijin kokarin wajen magance matsalar tsaron da ta addabi Najeriya.

A bayaninsa, Buhari yace yana fatan yan Najeriya zasu gane irin kokarin da sukeyi.

Buhari ya bayyana hakan ne a hira da manema labarai bayan halartan Sallar Idi a fadar shugaban kasa, Aso Villa, Abuja.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng