Gwamnan Yobe an angwance da diyar marigaryi Abacha, Hajiya Gumsu

Gwamnan Yobe an angwance da diyar marigaryi Abacha, Hajiya Gumsu

- Bayan mutuwar aurenta, diyar marigayi Janar Sani Abacha, Gumsu, ta sake aure

- Gumsu ta auri gwamnan jihar Yobe kuma shugaban rikon kwaryan jam'iyyar APC

- An yi taron daurin auren ne a gidan babban yayan Gumsu, Mohammad Abacha dake Abuja

Wani rahoton Daily Nigerian ya nuna cewa gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni a ranar Laraba, 14 ga afrilu ya auri matarsa ta hudu, Gumsu Sani Abacha.

Sabuwar Amaryar diya ce ga tsohon shugaban kasan mulkin Soja, marigayi Janar Sani Abacha.

A cewar rahoton, Buni wanda shine shugaban rikon kwaryan jam'iyyar APC ya bada kwabon zinari 24 matsayin sadaki.

An gudanar da taron daurin auren ne a birnin taraya Abuja, gidan babban yayan amarya, Mohammed Abacha.

DUBA NAN: Yan bindiga kai farmaki kwalejin Soji dake Kaduna

Gwamnan Yobe an angwance da diyar marigaryi Abacha, Hajiya Gumsu
Gwamnan Yobe an angwance da diyar marigaryi Abacha, Hajiya Gumsu Credit: @SalymBabajo
Asali: Twitter

KU KARANTA: Hotunan auren yar gwamnan Kebbi da tsohon kakakin majalisa, Hon. Dimeji Bankole

Gumsu, mai shekaru 45, a baya ta auri wani attajirin kasar Kamaru, Bayero Mohamadou, har tsawon shekaru 20 kafin suka rabu a 2020.

Daga cikin manyan da suka halarci taron akwai kwantrola janar na kwastam, Hameed Ali; kwamishanan yan gudun hijra, Bashir Garba-Lado, Sanata Lado DanMarke, dss.

Buni ya auri matarsa ta hudu bayan auren diyar magabacinsa, Adama Ibrahim-Gaidam, a shekarar 2019.

A bangare guda, tsohon kakakin majalisar wakilai Dimeji Bankole a ranar Juma'a 15 ga watan Janairu ya angwance da Aisha Shinkafi Saidu, diyar gwamnan jihar Kebbi, Atiku Bagudu.

Bankole, wanda ya rabu da matar sa ta farko a shekarar 2017, ya kasance mai matukar neman haihuwa cikin rukunin wadanda suka cancanta a ciki da wajen Najeriya.

Bikin auren rufe labule kan jita-jita dangane da niyyar aurensa tun bayan sakin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng