Allah ya yi wa tsohon gwamnan Kano, Isah Kontagora, rasuwa

Allah ya yi wa tsohon gwamnan Kano, Isah Kontagora, rasuwa

- Allah ya yi wa Kanal Aminu Isah Kontagora mai ritaya rasuwa

- Sakataren gwamnatin jihar Neja ne ya fitar da sanarwar rasuwar a yau Litinin

- Marigayin ya mulki jihohin Binuwai da Kano a yayin mulkin soja a Najeriya

Allah ya karba ran tsohon gwamnan jihar Kano, Aminu Isah Kontagora.

An tabbatar da rasuwar tsohon gwamnan bayan sakataren gwamnatin Neja ya bada sanarwar a wata takardar da ya fitar.

Marigayi Aminu Isah Kontagora ya rasu bayan gajeriyar rashin lafiya da yayi fama da ita a garin Abuja.

A lokacin rayuwarsa, ya taba mulkar jihohin Binuwai da Kano a yayin mulkin soja.

An haifa marigayin a shekarar 1956 kuma ya mulki jihar Kano daga watan Satumban 1998 zuwa watan Mayun 1999.

Allah ya yi wa tsohon gwamnan Kano, Isah Kontagora, rasuwa
Allah ya yi wa tsohon gwamnan Kano, Isah Kontagora, rasuwa. Hoto daga @BBCHausa
Asali: Twitter

Sojan mai mukamin Kanal ya mika wa farar hula ragamar mulki a shekarar 1999 zamanin mulkin shugaban kasa Janar Abdulsalami Abubakar.

Kamar yadda takardar sanarwar da sakataren gwamnatin Neja ya fitar, ya ce marigayin kamilin soja ne wanda za a dinga tunawa da shi saboda gudumawar da ya bada wurin cigaban jihohin Binuwai da Kano.

Tsohon gogaggen dan siyasan ya rike manyan mukamai kafin rasuwarsa.

KU KARANTA: Boko Haram sun kashe mutum 3, sun yi awon gaba da dabbobi a kusa da Maiduguri

A wani labari na daban, rundunar 'yan sandan jihar Yobe ta cafke wasu mutum 4 da ake zargi da hannu a mutuwar wata budurwa mai shekaru 18 a masaukin bakin gwamnatin jihar Yobe da ke Damaturu.

Premium Times ta gano cewa lamarin ya faru ne a ranar Alhamis. 'Yan sandan sun damke mutanen da ake zargi da hannu.

Majiya daga rundunar 'yan sandan ta ce babban wanda ake zargin shine wani mutum mai suna Al-bash Yahaya Ibrahim tare da wasu mutum uku.

An mika gawar matashiyar asibitin kwararru na jihar Yobe da ke Damaturu domin gano abinda ya kasheta.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel