Da duminsa: Ganduje ya bada umurnin rufe jami'ar Bayero da manyan makarantu a Kano

Da duminsa: Ganduje ya bada umurnin rufe jami'ar Bayero da manyan makarantu a Kano

- Bayan rufe sakandare, za'a rufe jami'o'in jihar Kano daga ranar Laraba

- Kwamishanar ilmin manyan makarantu ta sanar da hakan a jawabi

- Ana kyautata zaton za'a rufe makarantun saboda dawowar cutar Korona da kuma tsaro

Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje, ta bada umurnin rufe jami'ar Bayero da sauran makarantun gaba da sakandaren dake jihar ba tare da bata lokaci ba, rahoton Daily Trust.

Wannan sanarwan ya zo kwana daya bayan gwamnatin jihar ta kulle dukkan makarantun firamare da sakandaren dake jihar.

A jawabin da kwamishanar ilmin makarantun gaba da sakandare, Dakta Mariya Bunkure, ta rattafa hannu, an umurci dukkan dalibai su koma gidajensu.

"Muna shawartan dukkan dalibai su fita daga cikin makarantu daga ranar 16/12/2020," tace.

Gwamnatin jihar ta yi kira ga daliban su cigaba da bibiyan karatuttukansu yayinda suke zaune a gida.

KU KARANTA: Rashin tsaro da Korona: Jihohin Arewa 5 da suka rufe makarantunsu

Da duminsa: Dan sanda ya bindige mai babur, matasa sun bankawa ofishinsu wuta
Da duminsa: Dan sanda ya bindige mai babur, matasa sun bankawa ofishinsu wuta
Asali: UGC

KU KARANTA: Gwamna Matawalle ya kulle makarantun Zamfara dake makwabtaka da Katsina da Kaduna

A jiya mun kawo muku cewa gwamnan Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayar da umarnin rufe dukkan makarantun gwamnati da masu zaman kansu da ke fadin Jihar.

Gwamnatin jihar Kano ba ta bayyana dalilin rufe makarantun ba a cikin gajeriyar sanarwar da kwamishinan ilimi, Sanusi Kiru, ya fitar, kamar yadda Daily Nigerian ta wallafa.

"Mai girma gwamna ya bayar da umarnin gaggauta rufe dukkan makarantun gwamnati da masu zaman kansu ba tare da bata lokaci ba."

"Ana umartar iyayen da ke da yara a makarantun kwana su je domin dauko 'ya'yansu zuwa gida daga gobe, Laraba, 16 ga watan Disamba, 2020.

"Gwamnati ta na bayar da hakuri a bisa dukkan wani rashin jin dadi da daukan wannan mataki ya haifar," kwamishinan ya fitar.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel