An saki dan majalisan jihar Taraba da yan bindgiga suka sace

An saki dan majalisan jihar Taraba da yan bindgiga suka sace

- Bayan kwanaki a hannun masu garkuwa da mutane, dan majalisa ya samu kubuta

- Yan bindigan sun bukaci iyalinsa sun biya kudin fansan N150m

- Hukumar yan sandan ta tabbatar da sakin dan majalisan amma ba'a bayyana nawa a biya ba

Dan majalisar dokokin jihar Taraba, Bashir Bape, da aka yi garkuwa da shi ya samu yanci a daren Juma'a, majiya daga hukumar yan sanda da iyalansa sun tabbatar.

A cewar rahoton Premium Times, har yanzu ba a san ainihin adadin kudin da aka biya kudin fansa ba amma majiya daga gidan dan majalisan ya bayyana cewa: "an biya kudin fansa kafin aka sakeshi."

"An sake shi a daren jiya misalin karfe 10 na dare, kuma yanzu yana asibiti. Muna godiya ga dukkan wadanda suka taya mu addu'a," ya kara.

Yayinda aka tuntubi kakakin hukumar yan sanda a jihar, David Misal, ya tabbatar da lamarin.

"Mun tabbatar da cewa an sake shi," Misal yace.

Dubi ga yadda garkuwa da mutane ke yawaita a jihar, gwamnatin jihar ta haramta hawa babur a Jalingo da kewaye.

Kakakin gwamnan jihar, Iliye Bikye, ya ce an haramta hawa babur din ne saboda da babura ake amfani wajen aika-aika.

KU KARANTA: Yan ta'adda sun yi awon gaba da Ango da abokinsa bayan daurin aure

An saki dan majalisan jihar Taraba da yan bindgiga suka sace
An saki dan majalisan jihar Taraba da yan bindgiga suka sace
Asali: Twitter

DUBA NAN: Harin Kankara: Gwamna Masari ya kulle dukkan makarantun kwana a jihar Katsina

Mun kawo muku cewa wadanda suka sace Bashir Muhammed, dan majalisa a majalisar dokokin jihar Taraba, sun bukaci a biya naira miliyan 150 kafin su sake shi.

An sace Muhammed, wanda ke wakiltan mazabar Nguroje a karamar hukumar Sardauna da ke jihar, a gidansa da ke Jalingo a ranar Laraba, 9 ga watan Disamba.

A cewar rahoton, Muhammed ya roki shugabannin majalisar dokokin Taraba da gwamnatin jihar a kan su biya bukatar wadanda suka sace shi domin ceto rayuwarsa.

A cewar wata majiya a rahoton, mambobin majalisar sun hadu da Gwamna Darius Ishaku kan lamarin.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel