Hisbah ta kama dan sandan da ke sace yaran mutane domin lalata da su a Kano

Hisbah ta kama dan sandan da ke sace yaran mutane domin lalata da su a Kano

- Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama wani Basiru a wani gida yana lalata da wata yarinya mai karancin shekaru

- Mahaifin yarinyar ya ce ya nemi yarinyar sama ko kasa bai ganta ba na tsawon kwana 2, ashe tana wurin Basiru

- Hukumar ta na neman har da abokinsa, Jamilu, wanda ya gina gida musamman don yin lalata da mata

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama wani dan sanda Basiru a wuraren Rumawa da ke karamar hukumar Ungogo a kan laifin lalata, Vanguard ta wallafa.

Kamar yadda hukumar tace, an kama har da Basiru abokin Jamilu a wani daki da ke wuraren Rumawa, inda suka boye suna aikata alfashar.

Mazauna Rumawa sun yi gaggawar sanar da yadda Basiru da abokin sharholiyarsa suka makale a wani daki suna lalata da wata yarinya mai karancin shekaru, wacce iyayenta suka yi ta neman ta amma basu ganta ba.

KU KARANTA: A cikin sa'o'i 6, budurwa ta tashi daga Legas zuwa Benin kuma ta koma Legas a babur

Hisbah ta kama dan sandan da ke sace yaran mutane domin lalata da su a Kano
Hisbah ta kama dan sandan da ke sace yaran mutane domin lalata da su a Kano. Hoto daga thewhistle.com
Asali: UGC

Marikin yarinyar, Usman Ahmad ya ce ya yi ta neman diyarsa bai ganta ba, sai daga baya ya gano tana hannun hukuma.

"Basiru, abokin Jamilu ya gina gida a Rumawa musamman don yin lalata da kananan yara da sauransu.

"Na kan nemi yarinyata kwana biyu in rasa ta. Wannan karon na nemeta na kwana 2 ban ganta ba, ashe tana dakin wadannan mutanen," cewar marikinta.

Ya kara da cewa, "an kama Basiru da Jamilu, mai gidan da ake lalatar. Sannan an mayar da al'amarin a hannun 'yan sanda don su cigaba da bincike."

KU KARANTA: Da duminsa: Kotu ta janye belin Faisal Maina, ta bukaci a damko shi

A wani labari na daban, wani mutum mai suna Olumuyiwa Johnson, mai yara 2, ya tabbatar wa da wata kotu da take Ibadan cewa ba zai iya zama da matarsa ba.

A cewarsa, aurensa mai shekaru 24 ya kare da matarsa saboda rashin kamun kanta da barazana ga rayuwarsa.

Olumuyiwa, wanda mazaunin wuraren Eleta ne a Ibadan, ya tabbatar wa da alkali Ademola Odunade, cewa matarsa tana barazana ga rayuwarsa bayan ya gano tana lalata da wasu kusoshin cocinsu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng