KAI TSAYE: An tashi wasa, Nigeria 0-0 Sierra Leone (Wasan kwallon fidda gwanin gasar AFCON)

KAI TSAYE: An tashi wasa, Nigeria 0-0 Sierra Leone (Wasan kwallon fidda gwanin gasar AFCON)

Najeriya tana gwarawa da kasar Sierra Leone a wasar kwallon fidda gwanin gasar kasashen nahiyar Afrika da za'ayi a 2022.

Yan kwallon Super Eagles ne kan gaba da maki 7 a zaurensu bayan nasara kan Lesotho, Benin da kuma kunnen jaki da Sierra Leone.

Najeriya ta tashi 4-4 da Sierra Leone a wasar da aka buga a filin kwallon Sam Ogbemudia dake Benin City, jihar Edo ranar Juma'a.

Yanzu yan kwallon Super Eagles sun garzaya birnin Freetown, kasar Siera Leone domin buga wasa na biyu.

KAI TSAYE: Nigeria 0-0 Sierra Leone (Wasan kwallon fidda gwanin gasar AFCON)
KAI TSAYE: Nigeria 0-0 Sierra Leone (Wasan kwallon fidda gwanin gasar AFCON)
Asali: Getty Images

An tashi wasa Nigeria 0-0 Sierra Leone

An tashi wasan Najeriya da Sierra Leone babu wanda ya zura kwallo ko guda.

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng