Kiran 'yar majalisa karuwa: Alkali ya aike da dan majalisa gidan yari

Kiran 'yar majalisa karuwa: Alkali ya aike da dan majalisa gidan yari

- Cece-kuce ya barke, bayan an yankewa wani dan majalisa hukuncin zaman gidan gyaran hali

- An yanke wa Hercules Okoro hukuncin ne sakamakon zarginsa da akeyi da cin zarafi

- Kotu ta zargesa da cin zarafin mataimakiyar kakakin majalisa, duk da ya musa zargin

An yankewa dan majalisar jihar Imo, Hercules Okoro, mai wakiltar mazabar Ohaji Egbema, hukuncin zama a gidan gyaran hali akan laifin cin zarafi.

Legit.ng ta tattara bayanai akan yadda aka kama Okoro, dan majalisa a karkashin jam'iyyar APC, a ranar 13 ga watan Nuwamba, bayan wani rikici da ya barke tsakaninsa da mataimakiyar kakakin majalisar tarayya, Amarachi Iwuanyanwu.

An adana Okoro a gidan gyaran halin ne saboda laifuka 8 da ake zarginsa da aikatawa. Duk da dai bai amsa laifin da ake zarginsa da su ba.

Duk da lauyansa, Amandibuogu Osondu ya nemi belinsa amma abin yaci tura. A cewarsa laifin bai kai a dauresa ba. Alkalin, T Okee yace zai bukaci wani lokaci kafin ya duba yuwuwar bayar da belinsa.

KU KARANTA: Bani da budurwa saboda mata suna tsoron tsayi na, matashi mai kammala hidimar kasa

Kiran 'yar majalisa karuwa: Alkali ya aike da dan majalisa gidan yari
Kiran 'yar majalisa karuwa: Alkali ya aike da dan majalisa gidan yari. Hoto daga pmnewsnigeria.com
Asali: UGC

KU KARANTA: 'Yan sanda ba za su cigaba da kalmashe hannuwa ana kashesu kamar kaji ba, kwamishina

A wani labari na daban, karamin ministan fetur, Timipre Sylva, ya ce tashin farashin man fetur ya auku ne saboda wani kamfanin hada magunguna na Amurika, Pfizer ya bayyana riga-kafin cutar COVID-19.

Sylva ya fadi hakan ne a wata ganawar sirri da yayi da shugaba Muhammadu Buhari a Abuja ranar Lahadi, inda ya sanar da manema labarai cewa samun riga kafin cutar COVID-19 shine sanadiyyar tashin kudin man fetur a kasuwannin duniya.

"Tashin farashin man fetur ya auku ne sakamakon sanar da riga-kafin cutar COVID-19 da Pfizer sukayi. Idan an lura, farashin ya karu ne bayan sanar da samuwar riga-kafin" yace.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng