Babban abun alheri da ya taba samun Najeriya shine PDP, Atiku

Babban abun alheri da ya taba samun Najeriya shine PDP, Atiku

  • Najeriya ba ta da babban abokin alherin da ya wuce Jam'iyyar PDP, cewar Alhaji Atiku Abubakar
  • Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ne dan takarar kujerar shugaban kasa na PDP

Atiku Abubakar, tsohon mataimakin shugaban kasa, ya ce PDP ce babban abokin Najeriya.

Atiku ya ce PDP ta mulki Najeriya na tsawon shekaru 16 kafin APC ta amshi mulkin Najeriya a 2015, shafin Linda Ikeji ya wallafa.

Atiku ya wallafa hakan a shafinsa na kafar sada zumuntar zamani na Twitter, inda yace, "PDP ce babban abokin Najeriya. Duk bangarorin Najeriya suna bukatar jam'iyyar da za ta gyara Najeriya, ba wacce za ta lalata ta ba.

"Jam'iyyar PDP ta tabbatar da za ta gyara Najeriya, sannan ina rokon 'yan Najeriya da su amince da jam'iyyar don za ta tabbatar da adalci ga kowa."

Kara karanta wannan

Shahararen Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Shiga TikTok, Ya Bayyana Abin Da Zai Rika Wallafawa Kullum

Babban abun alheri da ya taba samun Najeriya shine PDP, Atiku
Babban abun alheri da ya taba samun Najeriya shine PDP, Atiku. Hoto daga @Lindaikeji
Asali: Twitter

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A wani labari na daban, Ali Ndume, sanata mai wakiltar kudancin Borno, ya ce da yawa daga cikin wadanda suke karkasin shugaban kasa Muhammadu Buhari barayi ne.

A ranar Lahadi, gidan talabijin din Channels sun yi hira da sanatan inda ya sanar da hakan, ya ce akwai mutanen da suke kokarin ganin bayan cigaba a mulkinsa.

Bayan an tambayeshi a kan yadda mulkin APC yake tafiya, cewa yayi gaskiya ba ya farinciki da tafiyar ta shekaru 5. Duk da suna yin iyakar kokarinsu, amma akwai gurabe da dama da ya kamata a cike.

A cewarsa, duk da kokarinsu, sai mutane sun zagesu, jaridar The Cable ta wallafa.

Ya ce shugaba Buhari sai dai ya bayar da umarni, amma ba zai iya zuwa yayi ayyuka da kansa ba, don haka mafi yawan matsalolin daga masu yin ayyukan ne.

Kara karanta wannan

Tinubu Ya Ba Wa Cocin Katolika Kyautan Naira Miliyan 20 A Wata Jihar Arewa

Asali: Legit.ng

Online view pixel