Karya ne, gwamnatin Buhari ba ta shirin biyan tubabbun yan Boko Haram N150,000 a wata, Bashir Ahmad

Karya ne, gwamnatin Buhari ba ta shirin biyan tubabbun yan Boko Haram N150,000 a wata, Bashir Ahmad

Hadimin shugaban kasa kan sabbin kafafen yada labarai, Bashir Ahmad, ya karyata maganar cewa gwamnatin Buhari na shirin fara biyan tubabbun yan Boko Haram N150,000 a wata.

Rahotanni sun nuna cewa gwamnatin Najeriya na biyan tubabbun yan Boko Haram albashi N150,000 a wata.

Amma Bashir Ahmad yace wannan labarin bogi ne kuma ya yi kira ga yan Najerita suyi watsi da hakan.

Ahmad ya bayyana hakan a shafinsa na Tuwita.

Yace: "Gwamnatin tarayya ba ta shirin fara biyan tubabbun yan Boko Haram kudi N150,000 a wata."

"Labari ne maras asali kuma na bogi."

Karya ne, gwamnatin Buhari ba ta shirin biyan tubabbun yan Boko Haram N150,000 a wata, Bashir Ahmad
Tubabbun yan Boko Haram Hoto: UGC
Asali: UGC

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng