Gwamnonin Arewa sun sha alwashin tabbatar da hadin kan Najeriya

Gwamnonin Arewa sun sha alwashin tabbatar da hadin kan Najeriya

- A ranar Litinin, 2 ga watan Nuwamba gwamnonin arewa suka yi wani taro a gidan Sir Kashim Ibrahim da ke Kaduna

- Ba gwamnoni kadai suka je taron ba, ministoci, manyan sarakuna, jami'an tsaro da sauran manyan mutane a arewa sun samu halarta

- Sun tattauna a kan duk wasu matsalolin arewa kamar zanga-zanga, ASUU, kafafen sada zumunta da yadda za'a shawo kansu

A ranar Litinin gwamnonin arewa suka yi kushe a kan zanga-zangar EndSARS, da kuma sauran al'amura da za su tayar da tarzoma, inda suka ce duk wanda ke neman canji bayan zabe to yayi zanga-zangar lumana.

Gwamnonin sun roki mutane da su hada kai da nuna kaunar juna tsakanin 'yan Najeriya, Vanguard ta ruwaito.

Sun fadi hakan ne a wata takarda da shugaban gwamnonin kuma gwamnan jihar Filato, Simon Lalong ya karanta bayan wani taro da suka yi a gidan Sir Kashim Ibrahim da ke Kaduna.

Gwamnonin Arewa sun sha alwashin tabbatar da hadin kan Najeriya
Gwamnonin Arewa sun sha alwashin tabbatar da hadin kan Najeriya. Hoto daga Vanguardngr.com
Asali: UGC

Sakataren gwamnatin tarayya, shugaban ma'aikatan shugaban kasa, ministoci, sarakunan arewa da sauran manyan mutane sun samu damar halartar taron.

KU KARANTA: Iyaye da 'yan uwa sun mayar da 'yan gidan fursuna 24 zuwa gidan kaso a Benin

Takardar da aka rubuta a ranar 2 ga watan Nuwamba ta kunshi abubuwa da dama wadanda za a yi don kawo cigaba a arewa. Inda suka mika jinjinarsu ga shugabannin gargajiya a kan babbar rawar da suka taka wurin dakatar da matasan arewa daga yin zanga-zangar EndSARS.

Sun tattauna yadda za su kawo hadin kai da cigaba a kasa. Sannan sun tattauna a kan yadda mutane ke yada labaran bogi a kafafen sada zumuntar zamani.

Sun tattauna a kan yadda za a sanya ido a babban birnin tarayya don gudun cigaba da lalata dukiyoyin gwamnati.

Sannan sun shawarci majalisar dattawa da su dinga hanzarin dakatar da duk wata zanga-zanga a cikin kasa. Kuma sun tattauna bukatar yin gaggawar daidaitawa da ASUU don dalibai su koma makarantunsu.

KU KARANTA: Namijin kishi: Fasto da mataimakiyarsa sun kone bayan saurayi ya ban ka wa gidan budurwa wuta

A wani labari na daban, Augustine Yiga, shararren faston nan na Uganda ya mutu, Jaridar The nation ta wallafa.

Faston ya rasu ne bayan watanni 5 da kama shi da laifin yayata cewa Coronavirus zazzabi ne wanda dama aka dade ana yinsa.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel