Amina Mohammed, Bande da sauran wadanda Tauraruwarsu ta ke haskawa a waje

Amina Mohammed, Bande da sauran wadanda Tauraruwarsu ta ke haskawa a waje

- Akwai wasu ‘Yan Najeriya da su ka samu manyan mukamai na Duniya

- Da dama daga cikinsu tsofaffin Ministoci ne da aka yi a gwamnatin kasar

- Wanda ake sa ran za ta zama sabuwar shiga a jerin ita ce Okonjo-Iweala

A cikin ‘yan shekarun bayan nan, an samu wasu mutanen Najeriya da ubangiji ya tsaga da rabonsu, su ka rike muhimman mukumai da ake ji da su a Duniya.

Wannan ruwan kujeru da aka yi wa ‘yan Najeriya ya zo ne a mulkin shugaba Muhammadu Buhari, wanda kasashen Duniya ke yi masa kallon dattijon kwarai.

Legit.ng Hausa ta kawo jerin wadannan zakakuran ‘yan Najeriya da su ke yin fice a waje.

KU KARANTA: Farfesa Tijjani Mohammed Bande ya samu kujera a UN

1. Amina J. Mohammed

Amina Mohammed mai shekaru kusan 60 ce mataimakiyar shugabar majalisar dinkin Duniya. Tsohuwar ministar ta hau wannan kujera ne a farkon 2017 bayan nada António Guterres.

Miss Mohammed ta ajiye kujerar Minista a Najeriya bayan ta samu wannan babbar kujera.

2. Tijjani Bande

A shekarar 2019 ne majalisar dinkin Duniya ta zabi wani mutumin Najeriya a matsayin shugaban zauren majalisa. Tijjani Bande ya sauka daga kan wannan kujera bayan shekara guda a 2020.

Farfesan ya fito ne daga jihar Kebbi, kafin nan shi ne wakilin Najeriya a majalisar dinkin Duniya.

KU KARANTA: Buhari ya shiga ganawar sirri da shugaban bankin AfDB

Amina Mohammed, Bande da sauran wadanda Tauraruwarsu ta ke haskawa a waje
Akin Adesina, Amina Mohammed, da Tijjani Bande Hoto: Hoto: Dailypost, GettyImages, UN
Asali: UGC

3. Akinwumi Adesina

Wani mutumin Najeriya da ke cikin wannan jeri shi ne Dr. Akinwumi Adesina wanda ya taba rike kujerar ministan gona da raya karkaka a lokacin da D. Goodluck Jonathan ya ke mulkin kasar.

Akinwumi Adesina ya zama shugaban bankin cigaban Afrika har kuma ya samu ya zarce.

4. Ngozi Okonjo-Iweala

Rahotanni sun kuma nuna cewa babu mamaki Ngozi Okonjo-Iweala ta zama shugabar kungiyar WTO. Babu wata mace ko mutumiyar Afrika da ta taba rike wannan kujera a tarihinta.

A halin yanzu kusan duka kasashen kungiyar Turai da Afrika su na goyon bayan Okonjo-Iweala.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel